Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Allah Shi Ya yi rayuwa kuma shi Ya yi mutuwa. Kowane mutum akwai lokacin haihuwar sa, akwai kuma lokacin mutuwarsa. Babban abin buƙata, shi ne cikawa da imani.
A rayuwar duniya, ana buƙatar mutum ya rayu cikin addini, kyautata wa iyali da dangi da maƙwabta da sauran abokan hulɗa a duk inda Allah Ya haɗa. A wannan tsari, marigayi Majidaɗin Galadiman Katsina ya samu shaidar kirki. Hakan ta tabbata, inda bayan rasuwarsa, mutane suka yi ta faɗar kyawawan halayensa tare da yi masa kyawawan addu’o’i.
Majidaɗin Galadiman Katsina ya rasu ne a ranar Asabar 14-10-1441 (Hijiriyya), 6-6-2020 (Miladiyya).
A yayin da muke tuna shi a yau, muna taya iyalansa da Galadiman Katsina, Malam Saddik Abdullahi Mahuta da dukkan al’ummar Malumfashi alhini.
Muna roƙon Allah Ya ji ƙan MAJIDAƊI, Ya yafe masa kurakuransa. Mu kuma da muka rage, Allah Ya sa mu cika da imani.









![Lost Heritage Series #1 – Mazari [Spindle]](https://i0.wp.com/taskargizago.com.ng/wp-content/uploads/2023/09/FB_IMG_1695164994735.jpg?resize=120%2C86&ssl=1)



