Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Dakarun Rundunar Sojojin Najeriya, Birged na Ɗaya sun kama ƙasurgumin ɗan ta’addar nan kuma madugun safarar makamai mai suna Baƙo Wurgi, wanda aka fi sani da laƙanin Baƙo Nagarba.
Kamar yadda fitaccen ɗan jarida, Zagazola Makama ya bayyana a rahotonsa, ya ce Baƙo, shi ne ake zargi da jagorantar kamu da kisan Mai Martaba Sarkin Gobir, marigayi Alhaji Isa Muhammad.

Kamar yadda rahoton ya bayyana, sojojin sun gudanar da samamen kama ‘yan ta’adda, a jiya Asabar da misalin ƙarfe 10 na dare. An rutsa da Baƙo ne a wani asibiti da ke garin Shinkafi na Jihar Zamfara, inda yake jinyar wani rauni da ya samu, sakamakon gumurzu da wata ƙungiyar ‘yan ta’adda ta daban.













