GARNAƘAƘl
——-
A rana irin ta yau, 08-06-2014 aka naɗa Sarki Muhammadu Sanusi II a karagar Sarautar Kano. A lokacin Bashir Yahuza Malumfashi ya rubuta wannan waƙe mai taken Garnaƙaƙi, domin mubaya’a da ƙarfafa baya:
——-
Ka riƙe Allah ka riƙe Manzo,
Ba za ka ga ƙasƙanci ba.
*
Ka daraja iyaye da mallammai,
Ba za ka ga tozarci ba.
*
Ka riƙe Ƙur’ani da Hadisi,
Ba za ka ganin talauci ba.
*
Wandara ka riƙe talakawa,
Jiddadun ba ka yi ƙaranta ba.
*
Ka riƙe gaskiya daɗa adalci,
Jigo ba za ka ga raini ba.
*
Ka zama limami ga limamai,
Ƙazgame ba zai ga bayanka ba.
*
Kai dai riƙa riƙo bisa himma.
Nasara ba ta yashe ka ba.
***













