Daga Wakilinmu
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa ya maida hannun kyauta, inda wata majiya ta shaida cewa wani mutum ya aika masa da kyautar firɗa-firɗan raguna guda 100 amma ya ƙi amsa.
Da yake bayyana yadda al’amarin ya faru, ɗan kishin ƙasa kuma mai tallafa wa marayu da marasa galihu, Malam Muhammad Aminu Kabir ya ce, a lokacin da saƙon ragunan ya kai ga Gwamna, “amma abin da ba kasafai ba, Gwamna Malam Umar Dikko Raɗɗa ya ce maza a maida ragunan daga inda suka fito, ba ya so. Ya yi faɗa sosai a kan lamarin,” in ji Malam Muhammad.
A yayin da yake nuna jin daɗinsa game da matakin da Gwamna Raɗɗa ya ɗauka, Malam Muhammad Aminu, addu’a ya yi masa, yana cewa: “Alhamdu lillah. Haka muke son Shugaba. Allah ya ƙara ba ka kariya Malam Ummaru, Allah Ya hana masu neman ka ta muguwar hanya samun ka, amin.”
A tsokacinsa, ya nuna ɓacin rai game da halayyar wasu masu hannu da shuni, waɗanda ba su taimaka wa mabuƙata na gaskiya. Ya ce “ga bayin Allah mabuƙata, ba za ku ba su ba, kuna tafiya inda za a ce kun yi. To ai yanzu sai ku yi abin da ya kamata, in kuma tarawa za ku yi sai ku je ku tara.”
Allah ya saka mashi da alheri
Amin Amin Ya Allah.
Innayi muku fatan alheri
Ma sha Allah. Muna godiya sosai.
Ma sha Allah. Muna godiya.
ALLAH ya kara daukaka
Haka ake son shugaba!.ina amfanin kyautar Riya