
Kwamishina Saulawa Jajirtacce Ne – Dr. Bala Nuhu
Shugaban Hukumar Yaƙi Da Ƙanjamau ta Jihar Katsina (KATSACA), Dokta Bala Nuhu, Sadaukin Kankiya ya bayyana cewa Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina, Dokta Bishir Gambo Saulawa mutum ne jajirtacce kuma mai kishin yi wa al’umma aiki.
Dokta Nuhu ya bayyana haka ne a jiya Laraba, a yayin wata ziyarar taya murna da ya jagoranci ayarin ma’aikatarsa suka kai wa sabon Kwamishinan na Ma’aikatar Lafiya, a ofishinsa da ke cikin Babbar Sakatariyar Jihar Katsina.
A yayin da yake gabatar da jawabinsa, Sadaukin na Kankiya ya ce, “mun kawo wannan ziyara ce domin taya ka murna, a kan wannan sabon muƙami da aka ba ka. Muna da tabbacin cewa Hukumar Lafiya a Jihar Katsina ta samu jajirtacce n shugaba, wanda zai yi aiki tuƙuru wajen ganin fannin lafiya ya ci gaba a Jihar Katsina.
Ya yi amfani da wannan ziyara kuma ya gatabatar da wasu buƙatu da suka shafi hukumar tasa ta yaƙi da cutar ƙanjamau (AIDS), domin inganta ayyukanta.
A nasa ɓangaren, da yake mayar da jawabi, sabon Kwamisinan na Lafiya, Dokta Saulawa ya yi farin ciki da wannan ziyara da hukumar ta kawo masa tare da ba su tabbacin cewa za a duba waɗannan buƙatu nasu, domin ci gaban harkar lafiya a wanan jjha.
Ya kuma yaba da ayyukan shugaban hukumar, bisa irin abubuwan ci gaba da hukumar take yi ƙarƙashinsa. Ya kuma yi addu’ar Allah Ya mayar da su gida lafiya.













