Daga Shanshani
Ina tsakar azabababben yawo da na saba, kawai sai ga ni a turance Malam Adam Ahmad Muhammed, Bakanon asali. Na iske shi yana ta zuba, da alamar yana cikin ɓacin rai. Ga abin da yake cewa:
Ko bajima ko badaɗe sai Filin Idin Kano ya canja muhalli.
Kasuwannin Kwari da Ƙofar Wambai sun cika sun batse kuma babu wani fili da za a iya faɗaɗa su sai Filin Idi.
Shi filin Idin da a wajen gari yake, amma yanzu ya zama a tsakiyar gari.
Shi filin Idin a da akwai filaye a zagayensa, yanzu kuma babu.
Duk lokacin da aka sami Gwamna mai kangado zai ɗauke filin zuwa wani filin da ya fi na yanzu yalwa, kamar Filin Mahaha!
Sannan a yi amfani da na yanzun wajen faɗaɗa kasuwannin nan guda biyu.
Ko a yanzu runfunan da aka gina ba ƙaramin taimaka wa ‘yan kasuwar filin ya yi ba.
Rushe su kuma da aka yi yanzu ba ƙaramin ƙuntata wa ‘yan kasuwar wajen ya yi ba.
In ba sa’a ba wani da shi da kasuwar sun yi bankwana ke nan, in ya yi sa’a ya sami wata harkar ko kuma ya koma jerin gwanon marasa aikin yi ke nan.
Aiki da hankali ya fi aiki da agogo!













