Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty
Wata majiya mai tushe ta tsegunta wa Taskar Gizago cewa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya aika wa Majalisar Dattijai da saƙon cewa ta cire sunan Hajiya Maryam Shatty daga jerin sababbin ministocin da ya aika mata domin tantancewa.
Maryam Shatty dai ta fito ne daga Jihar Kano.
Sai dai kuma ya zuwa haɗa rahoton nan, ba a bayyana dalilin cire sunan nata ba. Amma ana hasashen hakan ba zai rasa nasaba da ƙorafe-korafen da suka biyo bayan ambata sunan nata a matsayin Minista ba tun da farko.
Jama’a, mene ra’ayinku a kan wannan al’amari?












