Abubuwan Da Za Su Iya Faruwa Idan Kwankwaso Ya Koma APC
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Ya zuwa yanzu dai, Madugun Ƙungiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso yana ta janjanjeni-gidan-gwauro, yana nazarin ko ya canja sheƙa zuwa Jam’iyyar APC ko kuma ya yi zamansa a NNPP.
To amma shin me zai iya faruwa a da’irar siyasar Jihar Kano da ma ƙasa baki ɗaya, Idan ya zaɓi ya koma APC?
Idan har haka ta faru, to akwai hasashen cewa, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf shi da muƙarrabansa, su ma za su canja sheƙa zuwa APC.
Haka kuwa akwai yiwuwar adawar siyasa mai ƙarfi za ta kankama ta cikin gida a Jam’iyyar APC, tsakanin ƙungiyoyin Gandujiyya da na Kwankwasiyya.
A dai Jihar Kano ɗin, za a samu dusashewar taurarin wasu ‘yan siyasa, sannan a samu hasken wasu ya haskaka, musamman masu son takarar Gwamna, kamar irin su Sanata Barau Jibrin Maliya, Nasiru Gawuna da Murtala Sulen Garo da sauransu.
Haka kuma a dai Jihar Kano, APC za ta zama mafi girma da ƙarfi a siyasa.
A ɓangaren sarauta kuwa, akwai yiwuwar sake tsunduma cikin dabur-dabur a gidajen sarauta biyu da suka daɗe suna kai ruwa rana. Ana maganar ɓangaren Alhaji Aminu Ado Bayero da kuma Muhammadu Sanusi II.
A ƙasa kuma, ana ganin idan Kwankwaso ya koma APC, to adawa za ta kasance tsakanin Jam’iyyun APC da ADC, a yayin da PDP da LP za su zama ‘yan rakiya. Sauran al’amura kuwa sai lokaci zai zama alƙali.
Jama’ar Allah, ku a hasashenku, me kuke ganin zai iya canjawa a siyasance, idan Madugun na Kwankwasiyya ya canja sheƙa zuwa APC? Ku bayyana naku hasashen a Comment Section:
_______________













