• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Addini

Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Dr. Yunusa Zuba- Abuja

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 4, 2023
in Addini
0
Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Dr. Yunusa Zuba- Abuja

Zuma Rock da Haɗari. © Bashir Yahuza Malumfashi

28
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Huɗubar Jumu’a A Taƙaice Daga Masallacin Dr. Yunusa Zuba-Abuja

A yau Juma’a, 17-01-1445 (Hijriyya), 04-08-2023, Limamin Masallacin Dokta Yunusa da ke garin Zuba, Babban Birnin Tarayya Abuja, Liman ya buɗe huɗubarsa da basmala da godiya ga Allah da salati da sallama ga Manzon Allah, Sallallahu alaihi Wasallam.

Related posts

Duniya Ba Gidan Zama Ba

Duniya Ba Gidan Zama Ba

April 24, 2026
Mu Ji Tsoron Allah

Mu Ji Tsoron Allah

April 17, 2026

Maudu’in huɗubar ya karkata ne zuwa ga yanayin ƙunci da wahala da talauci da tsananin rayuwa da al’umma ke ciki. Malam ya jawo hankalin al’umma da mu fahimci yanayin da ake ciki na tsadar rayuwa, inda wasu ke kwana da yunwa kuma su tashi da yunwa. Mutane na fuskantar barazanar talauci. Ga marasa lafiya kuma ba su da abin sayen magani.

Malam ya buƙaci al’umma da mu kasance masu taimakon juna. Ya ce kowa ya kalli na kusa da shi, ya taimaka wa wanda yake da buƙata da abin da Allah Ya hore masa, komai ƙanƙantarsa.

Malam Ya ce akwai fa’ida sosai a taimakon mabuƙaci. Mu kasance masu ƙoƙarin yaye wa ‘yan uwanmu wata damuwa da suke ciki. Kuma mu sani, duk wanda ya cire wa ɗan uwansa wata damuwa, shi ma Allah zai cire masa tasa damuwar, duniya da lahira.

Malam ya nemi da mu kasance ‘yan uwan juna, mu kare haƙƙoƙin juna. Ya ce Musulmi ɗan uwan Musulmi ne, a lokacin da yake raye da kuma bayan mutuwarsa. A lokacin da yake raye, yana da haƙƙin ka kula da shi, ka taimake shi a lokacin da yake buƙatar taimako. A lokacin da ya mutu kuwa, yana da haƙƙin ka yi masa addu’a.

Malam ya kawo hadisin da ke ƙarfafa muhimmancin taimakon juna, wanda ke cewa lallai Allah yana taimakon bawa, madamar bawa yana taimakon ɗan uwansa.

“Duk wanda ke son dacewa a duniya da lahira, to ya lizimci taimakon ɗan uwansa. Don haka mawadata su taimaka wa mabuƙata, Allah zai taimake su.

Malam Ya rufe huɗubarsa da addu’a, Allah Ya kawo mana sauƙi, Ya ba mu damina mai albarka.

Amin summa Amin!

Previous Post

Madakin Zazzau Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Hakimin Basawa

Next Post

Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

Related Posts

Duniya Ba Gidan Zama Ba
Addini

Duniya Ba Gidan Zama Ba

April 24, 2026
Mu Ji Tsoron Allah
Addini

Mu Ji Tsoron Allah

April 17, 2026
MARTABAR MANZON ALLAH (SAW)
Addini

MARTABAR MANZON ALLAH (SAW)

April 13, 2026
Next Post
Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

Tinubu Ya Ƙwace Muƙamin Minista Daga Maryam Shatty

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

MALUMFASHI: MUN YI RASHIN ABOKI KUMA ƊAN UWA

MALUMFASHI: MUN YI RASHIN ABOKI KUMA ƊAN UWA

July 19, 2024
Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

November 24, 2025
Katsina State at 37: Reflecting on Successes, Challenges, and the Way Forward

Katsina State at 37: Reflecting on Successes, Challenges, and the Way Forward

September 23, 2024
2027 and the Rise of a Third Force: Can ADC’s Political Heavyweights Unseat Tinubu?

SHIN KO GAMAYYAR ‘YAN ADAWA NA JAM’IYYAR ADC ZA SU IYA KADA TINUBU A 2027?

July 3, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.