• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Wednesday, June 17, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Siyasa

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

SIYASA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 17, 2026
in Siyasa
0
Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

Jaafar ya buɗe wa 'yan Kwankwasiyya idanu

19
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya
__________
Fitaccen ɗan jarida kuma mawallafin jaridar Daily Nigerian (online), Jaafar Jaafar, ya gabatar da wani tsokaci mai ban mamaki, a shafinsa na Facebook, dangane da matakin da Jam’iyyar NDC a Jihar Kano ta ɗauka; inda ta ayyana Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, a matsayin wanda zai zama Mataimaki ga ɗan takarar Gwamna a Jihar ta Kano.

Tun da farko, Malam Jaafar ya buɗe bayanin nasa da kaushin harshe, inda ya ce: “Ɗaukar Mustapha Kwankwaso a “Deputy Governor” ba daidai ba ne. Haƙƙi ne a gare mu, mu faɗi gaskiya duk inda muka gan ta. Kujerar “Deputy Governor” ba abar wasa ba ce.

Related posts

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

April 9, 2026

“Yau in Allah ya ɗauki ran Gwamna, Deputy za a rantsar ya maye gurbinsa. Kujera ce wacce gogaggun mutane irin su B.B. Faruk, Audu Dawakintofa, Wada Abubakar, Professor Hafiz Abubakar da sauransu suka riƙe.

Jaafar ya buɗe wa ‘yan Kwankwasiyya idanu

Ɗan jaridar, wanda ya yi fice wajen bankaɗo bahallatsar ‘yan siyasa, ya ci gaba da cewa: “Amma a haƙiƙanın gaskıya ɗaukar Mustapha a matsayin “Deputy Governor” ya saɓa da duk shika-shikan Ɗarikar Kwankwasiyya. Ni a karan kaina, Mustapha yana mutunta ni kuma ko a yanzun nan da nake wannan rubutu, na ga ya kira ni a waya. Idan maslahata zan duba, ba ni da matsala da shi. Amma a kan abin da ya shafi al’umma, ina da matsala da shi.”

Da yake magana game da halayen Mustapha Kwankwaso, Jaafar ya bayyana cewa: “Ba wai ina so na aibata Mustapha ba ne amma duk wanda ya san Mustapha ya san bai cancanci wannan kujera mai girma ba. Walau a fannin Boko ko Muhammadiyya ko mu’amula, babu inda za a ce Mustapha ya kere duk zaƙakuran mutanen da suka yi shekara da shekaru suna hidimta wa tafiyar Kwankwasiyya.”

Ya ci gaba da cewa: “Ko shi kansa Oga, a duk harkokin da yake yi na sana’a, ban ga ɗaya da Mustapha ne ke kula da ita ba. Ko manajan gona bai ba shi ba amma kuma yau a ɗora shi a gwadaben da zai yi “managing” dukiya da rayukan miliyoyin al’umma?”

Daga ƙarshe dai, babban ɗan jarida Jaafar ya ƙarƙare bayaninsa da gargaɗi da kuma neman Jam’iyyar NDC da shugabanninta da su gyara lamarin, inda ya ce: “A gyara lamarin nan, kada garin neman gira a rasa ido.”

Abin tambaya a nan shi ne, ko iyayen Jam’iyyar NDC a Jihar Kano za su ɗauki shawarar Jaafar da sauran ‘yan Kwankwasiyya da suke ganin ba a yi masu daidai ba? Lokaci ne kawai zai nuna haka.

Jama’a masu karatu, shin yaya kuke ganin wannan lamari, mene ne ra’ayinku? Ku bayyana a Comment Section.
__________

Previous Post

Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

Related Posts

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi
Siyasa

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC
Siyasa

Najeriya 2027: Yadda ADC Za Ta Murƙushe APC

April 9, 2026
2027: SABUWAR GUGUWAR SAUYIN SIYASA A KANO
Siyasa

2027: SABUWAR GUGUWAR SAUYIN SIYASA A KANO

February 24, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Gwamnan Jigawa Ya Kama Ma’aikatan Asibiti Suna Sayar Da Magungunan Gwamnati

Gwamnan Jigawa Ya Kama Ma’aikatan Asibiti Suna Sayar Da Magungunan Gwamnati

July 5, 2023
Ba Mu Da Wata Ƙasa Kamar Najeriya

Ba Mu Da Wata Ƙasa Kamar Najeriya

November 4, 2025
The Federal Capital Territory Abuja: The Past, Present and the Future

The Federal Capital Territory Abuja: The Past, Present and the Future

September 13, 2023
Ƙuncin Rayuwa: Matasa Ku Tashi Ku Nemi Ilimi Da Sana’a – In Ji MAK

Ƙuncin Rayuwa: Matasa Ku Tashi Ku Nemi Ilimi Da Sana’a – In Ji MAK

August 15, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya
  • Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa
  • BARKA DA SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI 1448 HIJIRIYYA

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

June 17, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

June 16, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.