RAYUWA
__________
Ni Bashir Yahuza Malumfashi, na sadaukar da wannan waƙe ga ɗaukacin TALAKAWAN NAJERIYA, bisa halin matsi da jarabawa da ake ciki. Allah kawo sauƙi da sawaba – Amin!
__________

Komai wuya ko akasi,
Kar ka yi kukan matsatsi,
Kar ka zamo mai taratsi;
Ka yi godiya ko ba hatsi,
Rabbi Allah bai mance ka ba.
Idan ka samu dami ɗaya,
Waiga ƙasa wani ba ɗaya,
Wani bai da ko da ‘yar tiya,
Sai dai ya je yai magiya.
Ƙarfin jiki ba ka kai shi ba.
Kai ne kake da ƙafa biyu,
Har ka ƙara da ido biyu,
Ga hannuwanka guda biyu,
Ka ɗauki saiti biyu-biyu.
Rahama ta Allah ba mutum ba.
Wani ko ƙafarsa guda ɗaya,
Wani ko idonsa guda ɗaya,
Wani babu hannu ko ɗaya,
Bai da tsaba ƙwaya ɗaya,
Iko na Allah ba na su o’o ba.
Wani ga gida tangameme,
Filin noma wangameme,
Dokin hawa sangameme,
Ga tulun ciki sunƙumeme,
Komai ya biɗa bai rasa ba.
Ga wata can kanta gashi,
Ya yi kwance ya yi laushi,
Kowa ya taɓa ya ji taushi,
Kowa ya gani zai murmushi,
Hikima ta Allah ba wanin ba.
Wata kanta sai yai kamar bal.
Babu gashi ƙwal yake tal.
Doguwa ce ga ta shantal,
Wata kau gajera ce ‘yar gajal.
Halittar Allah ba ta gaza ba.
Wani yai gabas wani yamma,
Wani dariya wani hamma,
Wani kasala wani himma,
Suturar wani ta yi tsumma.
Kowa da inda ya sa gaba.
Wani kam ɗan kasuwa ne,
Wancan kuwa ma’aikaci ne,
Shi ɗan uwa kafinta ne,
Ga wani nan injiniya ne,
Rayuwa ce ba ta zam ɗaya ba.
‘Yan uwana sai mu gane,
Rayuwa dai kar mu gune,
Godiyar Allah mu manne,
Komai ka gani ƙalubale ne,
Allah Yake yi ba mutum ba.
Ni Bashiru na gode Allah,
Ni ɗan Yahuza ba ni gilla,
Na Malumfashi ba ni illa,
Fasihin Galadima aƙalla.
Kariyar Allah ba mutum ba!
__________
© Bashir Yahuza Malumfashi
Talata 19-02-1445 (Hijiriyya),
05-09-2023 (Miladiyya).
__________













