Namu Ya Samu: Kira Da Shawara Ga DCG #Abdulbasir_Hamisu
Daga Abdul’aziz ibni Abdul’aziz
Alhamdu lillah! Ma sha Allah!
Mutanen Malumfashi, mu tashi tsaye mu taya ɗan uwanmu murna, Allah yya kai shi mataki na ƙarshe a aikin Kwastam. Muna magana game da Deputy Comptroller General Abdulbasir Hamisu.
Sai dai kuma duk da ina alfahari da wannan kujera da Allah Ya ba ka, bai hana in jawo hankalinka, cewa duk bayan kwana ɗaya kana matsar aje aiki saboda haka kuma idan ka aje aiki dole za ka so mu’amala da mutanen gida ko kuma idan kana da hali ma ka ce za ka jarraba siyasa, koda irin ta ‘yan shan kai ce, wato ka bi short cut.
Bisa ga haka, ga wasu ‘ yan shawarwari da zan ba ka:
1-Ka tuna cewa Jamilu Tukur, lakanin da ake masa shi ne “Jamilu Mai Offer.”
2-Yakubj Joker, laƙanin da ake masa shi ne “Jikan Jaba Hantsi Ka Leƙa Gidan Kowa.”
3-Hussaini Mahuta, ana kiran shi da “Husaini Mai INEC.”
4-Babangida Hada, ana kiran shi da “Mai Matasan ‘Yan Sanda” a Malumfashi.
5-Justice Sadiƙ Abdullahi Mahuta ya ɗauki kananan ma’aikata a kotu sosai.
Akwai sauran waɗanda ban iya zayyana sunayensu ba a Malumfashi. Don Allah ka yi ƙoƙari ka ga cewa kai ma bayanka ta yi kyau a aikin Kwastam. Kada ka yi irin na wasu mutane guda biyu ‘yan Gangarawa, waɗanda Allah Ya ba su dama amma duk Malumfashi babu mutum ukku waɗanda suka ɗauka aiki ko kuma suka gina su a matsayin yaransu a Malumfashi ko kuma Jihar Katsina baki ɗaya.
Allah Ya sa shawarata ta isa gare ka. Kuma ina roƙon waɗanda suke iya isar maka da wannan saƙo, su taimaka mani su isar maka da shi don Allah.
~~~~~~~
Abdulaziz ibnu Abdulaziz, shi ne Sarkin Samarin Galadiman Katsina-1 kuma Sardaunan Matasan Malumfashi.
~~~~~~~













