Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Sojoji Sun Cafke Manyan Dillalan Miyagun Ƙwayoyi

Sojojin Bataliya ta 192 sun kama wasu muggan dillalan miyagun ƙwayoyi, a yayin da suka tare wata babbar mota maƙare da buhunhuna 397 da ke ƙunshe da ganyen da ake kyautata zargin tabar wiwi ce.
Kamar yadda Daraktan Watsa Labarai na Rundunar Sojojin Nigeria, Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya bayyana wa manema labarai, ya ce sojojin sun kama motar ce a jiya Talata, a yayin da take tafiya zuwa garin Sango Otta a Jihar Ogun. Binciken farko ya nuna cewa sun ɗauko ganyen ne daga ƙasar Ghana, suka biyo ta Jamhuriyyar Benin zuwa Igholo-Idiroko domin isa Sango Otta.
Mutanen da aka kama ɗauke da kayan laifin sun haɗa da Mista Matthew Edegbe, ɗan ƙasar Benin da Mista Joshua Dansu, mazaunin Idiroko. Dukkansu suna hannun hukuma, suna fuskantar bincike.
Tuni dai sojojin suka tattara waɗanda ake zargin da motar da kayan, suka miƙa su ga Hukumar Yaƙi Da Tu’ammali Da Muggan Ƙwayoyi (NDLEA) da ke Shiyyar Lagos, domin ci gaba da bincike.
Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Nigeria, Manjo-Janar Taoreed Lagbaja ya yaba wa sojojin da suka gudanar da wannan aiki, sannan ya buƙaci su ƙara ƙaimi wajen kakkaɓe dukkan muggan iri daga ƙasar nan gaba ɗaya.













