• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Thursday, January 22, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Bayan Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihar Katsina: Ya Kamata A Tallafa Wa Iyalan Mutanen Da Aka Tarwatsa

TSOKACI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
October 15, 2025
in Gizago
0
Bayan Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihar Katsina: Ya Kamata A Tallafa Wa Iyalan Mutanen Da Aka Tarwatsa

Ya kamata a tallafa wa 'yan gudun hijira da iyalan mamatansu

51
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Bayan Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihar Katsina: Ya Kamata A Tallafa Wa Iyalan Mutanen Da Aka Tarwatsa

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)

January 17, 2026
Ya kamata a tallafa wa ‘yan gudun hijira da iyalan mamatansu


                              •••••••

A halin yanzu, bayan tattaunawa da sulhu da ake yi da ‘yan bindiga a wasu yankunan Jihar Katsina, akwai buƙatar gwamnatin jiha, a ƙarƙashin adalin Gwamna, Dokta Dikko Umar Raɗɗa, ta karkata hankali wajen kula da mutanen da suka fi fuskantar illar wannan rikici.

Duk da cewa manufar sulhu ita ce kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali, akwai daruruwan iyalai da suka rasa komai, daga rayuka, gidaje har zuwa dukiyoyi, waɗanda har yanzu ba su dawo hayyacinsu ba. Wannan rukuni na jama’a, bai kamata a manta da su ba a lokacin da ake ƙoƙarin gina sabon tsarin zaman lafiya.

Gwamnatin Jihar Katsina tare da shugabannin ƙananan hukumomi, ya kamata su taka wata rawar gani wajen shirya wani shiri na musamman domin tallafa wa waɗannan iyalai. Misali a Ƙaramar Hukumar Malumfashi, akwai marigayi ASP Ɗahiru, wanda a kwanakin baya ‘yan bindiga suka kama, ya kwashe tsawon lokaci a hannunsu, sannan suka raba shi da rayuwarsa kuma suka hana iyalansa gawarsa. Bayan shi, akwai wasu da dama a sassa daban-daban na jihar.

Ga mutanen da aka tarwatsa ƙauyukansu, tallafi gare su bai kamata ya tsaya ga kayan abinci kaɗai ba. Ya dace a haɗa da sake gina gidajen da suka ƙone, ba da jari ga mata da matasa da suka rasa hanyar samun abin dogaro da kuma shirye-shiryen ilimi da kiwon lafiya ga yara da tallafi na musamman ga tsofaffi. Hakan zai tabbatar da cewa waɗanda suka tsinci kansu cikin wahala sakamakon ta’addancin ‘yan bindiga, ba za su zama masu tabbata cikin rayuwar zaman gudun hijira a ƙasarsu ba.

Haka kuma, akwai buƙatar a kafa wani kwamitin kulawa da farfaɗowar al’umma, wanda zai duba yankunan da aka fi lalatawa, tare da nazarin hanyoyin da za a dawo da su cikin tsarin rayuwa mai ma’ana. Wannan kwamitin zai ƙunshi jami’an gwamnati, shugabannin al’umma, malamai da ƙungiyoyin agaji, domin tabbatar da cewa tallafin da ake bayarwa ya isa ga waɗanda suka fi buƙata, ba tare da nuna son kai ko fifiko ba.

Bugu da ƙari, gwamnati ta kamata ta samar da hanyoyin tsaro da sa ido a yankunan da aka ƙulla sulhu, domin kauce wa sake dawowar ‘yan bindiga. Mutanen da aka tilasta barin gidajensu su samu tabbaci cewa idan suka koma, za su rayu cikin aminci. Wannan mataki ne da zai ƙarfafa imani da gwamnati kuma ya rage yuwuwar komawar wasu cikin ‘yan gudun hijira ga hanyoyin laifi saboda matsin tattalin arziki.

Har kullum dai ya kamata mu san cewa, sulhu ba zai cika ba idan ba a kula da waɗanda suka shiga matsala a sakamakon harin ‘yan bindiga ba. Zaman lafiya na gaskiya yana nufin dawo da martaba da mutuncin rayuwar al’umma. Don haka, kira ga gwamnatin Jihar Katsina da shugabannin ƙananan hukumomi shi ne, a gaggauta samar da shirin tallafi na musamman ga iyalan da aka tarwatsa, domin su samu ƙarfin gwiwa, su bar bara da gudun hijira, su koma zama ‘yan ƙasa masu alfahari da ƙasarsu.
_______________

Previous Post

TARON MALUMFASHI FACEBOOK CONNECT: YUNKURIN BUNKASA MALUMFASHI DA KEWAYE (8)

Next Post

BAKIN JAƁA (7)

Related Posts

My 83rd Birthday and the Kindred Spirit
Gizago

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (9)

January 17, 2026
Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)
Gizago

Yunkurin ‘Yan Ba-Zata/Hausawan Bogi Na Haddasa Ruɗani A Arewa (8)

January 13, 2026
Next Post
BAKIN JAƁA (7)

BAKIN JAƁA (7)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Sharhin Littafin Faɗakarwa Dangane Da lllar Miyagun Ƙwayoyi

Sharhin Littafin Faɗakarwa Dangane Da lllar Miyagun Ƙwayoyi

December 24, 2024
SASSANYAN AMINCI (2)

SASSANYAN AMINCI (2)

September 5, 2025
Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

Mawaƙi Kizz Daniel Ya Amshi Musulunci

January 3, 2026
CANJIN ZAMANI: Rayuwar Mata A Ƙarni Na 21

CANJIN ZAMANI: Rayuwar Mata A Ƙarni Na 21

January 7, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)
  • Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya
  • Nazari, Tsokaci Da Sharhin Littafin Tarkon Mut’a

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (1)

January 21, 2026
My 83rd Birthday and the Kindred Spirit

Cikar Shekaru 83 A Duniya: Ranar Da Na Ga Zumunci Da Fatan Alheri Daga Masoya

January 19, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.