Daga Junaidu Amadu Doro
Sababbin Kwamishinoni Sun Bayyana A Jihar Katsina
A yau Laraba Majalisar Dokoki a Jihar Katsina ta byyana sunayen Kwamishinoni guda 20 da Gwamna Malam Umaru Dikko Radda ya aika mata.
A zaman majalisar na yau, Shugaban Masu Rinjaye, Hon. Shamsuddeen Abubakar Dabai shi ne ya bayyana sunayen kwamishinonin, a wata takardar saƙo da Gwamnan ya aika mata.
Sababbin Kwamishinonin su ne kamar haka:
1-Farfesa Ahmed Muhammad Bakori, daga Ƙaramar Hukumar Bakori.
2-Hon. Ishaq Shehu Dabai, daga Ƙaramar Hukumar Ɗanja.
3-Farfesa Badamasi Lawal Charanci, daga Ƙaramar Hukumar Charanci.
4-Dokta Nasiru Mu’azu Ɗanmusa, daga Ƙaramar Hukumar Ɗanmusa.
5-Malam Bala M. Salisu, daga Ƙaramar Hukumar Zango.
6-Farfesa Abdul Hamid Ahmed, daga Ƙaramar Hukumar Mani.
7-Hon. Musa Adamu Funtua, daga Ƙaramar Hukumar Funtua.
8-Alhaji Yusuf Rabi’u Jirdede, daga Ƙaramar Hukumar Mai’aduwa.
9-Hon. Aliyu Lawal Zakari, daga Ƙaramar Hukumar Dutsi.
10-Hon. Bishir Tanimu Gambo, daga Ƙaramar Hukumar Dutsinma.
11-Hon. Hamza Suleiman Faskari, daga Ƙaramar Hukumar Faskari.
12-Alhaji Isa Muhammad Musa, daga Ƙaramar Hukumar Ƙanƙara.
13-Injiniya Dokta Sani Magaji Ingawa, daga Ƙaramar Hukumar Ingawa.
14-Dokta Faisal Umar Kaita, daga Ƙaramar Hukumar Kaita.
15-Alhaji Bello Husaini Kagara, daga Ƙaramar Hukumar Ƙafur.
16-Hajiya Hadiza ‘Yar’adua, daga Ƙaramar Hukumar Katsina.
17-Hajiya Zainab M. Musawa, daga Ƙaramar Hukumar Musawa.
18-Alhaji Musa Na Habu, daga Ƙaramar Hukumar Daura.
19-Dokta Bishir Gambo Saulawa, daga Ƙaramar Hukumar Katsina.
20-Barista Fadila Muhammad Dikko, daga Ƙaramar Hukumar Kurfi.













