• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, June 23, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

TSOKACI/NAZARI

Fatuhu Mustapha by Fatuhu Mustapha
June 22, 2026
in Gizago
0
Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Malam Fatuhu Mustapha, marubucin tsokacin

6
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Daga Fatuhu Mustapha
__________

Related posts

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

June 23, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

June 16, 2026
Malam Fatuhu Mustapha, marubucin tsokacin

Saint Luis da Saint Thomas: Kalubale ga Ƙadiriyya, Shia, Izala da Tijjaniya. Ina ta mamaki da wasu malamai suka fara hawa mumbari suna ɓaɓatu a kan wai, suna mamaki ya aka yi gari kamar Kano amma Musulmi ke kai ‘ya’yansu makarantar Kiristoci!

Amma ai ba wannan ya kamata su tuhuma ba. Shekara sama da 700 ana Ƙadiriyya a Kano. A nuna min ƙwaƙƙwarar makarantar boko koda guda ɗaya da ‘yan Ƙadiriyya suka kafa a Kano, ko ma a wani wuri domin ‘ya’yan ‘yan ɗariƙar su samu ilmin boko mai kwari. A lura, ban ce babu ba fa, ban san da ita ba ne! Je ka Bagadaza ka ga irin makarantun bokon da ‘ya’yan Ƙadirawa suke zuwa.

Tun kafin zuwan Shehi Ibrahim Nyass, a shekarar 1920 ake Tijjaniya a Kano amma a yau sama da shekara 100 da zuwan Shehu Ibrahim, ba mu da ƙwaƙƙwarar sakandare da za mu nuna wa duniya, wadda take yaye ‘yan Tijjaniya, su samu karatun boko mai inganci! Je ka Morocco ka ga irin makarantun da ‘ya’yan Tijjanawa ke zuwa. Ƙasar Morocco tna ware kashi 1/5 na kasafin kuɗinta, domin bayar da ilmi kyauta kuma dole ga ‘yan ƙasar.

Izala ta haura shekara 40 da kafuwa, ta doshi 50 yanzu. Kuma a iya kiranta da ‘ya’yan nan da Turawa suke ce wa, “born with golden spoon.”. A nuna min makaranta kamar Saint Luis guda ɗaya da suka kafa, wacce take samar wa ‘ya’yan mabiyansu, ƙwaƙƙwaran ilmin boko. Kusan da yawansu sun je Saudi karatu. Haka suka ga ana yi wa ilmin boko a can?

Ina ‘yan Shi’a? Ba fa muzahara ce kawai aikin Shi’a ba. Babban abin da ya sa Shi’a ta yi zarra, duk da rashin yawansu, in an kwatanta da Sunni, amma kuma saboda jahircewarsu a fannin ilmi, ya sa yau ƙasar da ita ce karfin Shi’a a duniya, ta zama gagara-gasa a duniya, wato kasar Iran.

An kafa Sakandaren Saint Luis da Saint Thomas a Kano tun a shekarar 1951, sama da shekaru 70 ke nan a yanzu. Kuma tun lokacin makarantar ba ta taɓa yadda ta yi ƙasa a gwiwa wurin bai wa yara ilmi mai inganci ba. Saɓanin yadda muka bari, namu makarantun suka lalace, suka koma bai wa yara ilmi mara inganci.

Bari mu ɗau darasi daga Musulmin Yarabawa, waɗanda muke yi wa kallon cewa mun fi su zama Musulmi. A lokacin da kusan makarantun boko a ƙasashen Yarabawa kusan kashi 70 na ‘yan Mishan ne, sai aka lura da yadda suke ɗora wa ‘ya’yan Musulmi ƙa’idoji masu tsauri, kafin su yadda su ɗauke su a makarantun. Don haka, a 1943, srishararren Lauyan nan kuma Ministan Yaɗa Labarai a Jamhuriyya ta farko, Alhaji Thanni O.S. Benson, da haɗin gwiwar wasu mutum biyu, suka kafa Kungiyar Ansaruddeen, domin su tabbatar sun bai wa ‘ya’yan Musulmi ilmin zamani mai nagarta, ba tare da an tsangwame su ba.

Sun fara kafa ta farko a Isolo daga nan suka ci gaba da kafa makarantu saboda ‘ya’yan Musulmi su samu ingantaccen ilmi. Waɗannan makarantu sun taimaka wa ‘ya’yan Musulmi a ƙasar Yarabawa. Sun yi kafaɗa da kafaɗa da ‘ya’yan kiristoci da a da suke musu wani gani-gani.

A zagaya, a Arewa da muke kallon mu ne Musulmi na gaske fiye da Yarabawa, a nuna min fitacciyar makarantar boko da wata ƙungiyar addini a Arewa ta kafa kuma ta ɗore har zuwa yau. Makaranta ɗaya da walau Ƙadiriyya, Tijjaniya, Izala ko Shi’a ta kafa, domin ta samar da injiniyoyi, lauyoyi, kafintoci, likitoci da sauransu.

Zan so mutane su nemi ƙasidar Dr. Bala Usman da Alkasim Abba, mai taken “Political Economy of Political Instability: Facing Reality in 7 Northwestern States.” A nan za mu fahimci irin mummunar fahimtar da muka yi wa ilmi a addinin Musulunci.

Allah ya ganar da mu!
___________

Previous Post

Maryam ‘Yar Aljanna (2)

Next Post

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

Related Posts

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo
Gizago

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

June 23, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa
Gizago

Taɓarɓarewar Tsaro A Najeriya: Janar Buratai Ya Buƙaci A Ɗauki Matakan Gaugawa

June 16, 2026
A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?
Gizago

A Yayin Da Aka Kashe Janar Saura Wa Kuma Ya Rage?

June 14, 2026
Next Post
Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara 'Yar Tuwo-Tuwo

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Rasheedah Tana Wa Al’umma Barka Da Sallah

Rasheedah Tana Wa Al’umma Barka Da Sallah

June 29, 2023
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (2)

February 25, 2026
TSOKACINMU NA YAU – 01

TSOKACINMU NA YAU – 01

March 1, 2025
EFCC Ta Kai Farmaki Jihar Katsina

Gamayyar Ƙungiyoyin Tsofaffin Ɗalibai Sun Roƙi Gwamnan Katsina Ya Girke Jami’ar Kimiyyar Lafiya A Malumfashi

June 27, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo
  • Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa
  • Maryam ‘Yar Aljanna (2)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

Tattaunawar Ɗan Jarida Da Bazawara ‘Yar Tuwo-Tuwo

June 23, 2026
Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

Ilimin Zamani: Babban Ƙalubale Ga Al’ummar Musulmin Arewa

June 22, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.