Daga Shanshani
Jiya ina kallon talabijin, na murɗo tashar Channels sai na ga ana tattaunawa da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Umar Abdullahi Ganduje.
Daga yadda na ga Ganduje na kumfar baki, fuskarsa murtuk kamar kunun kanwa, nan na tabbatar da cewa lallai akwai matsala.
Yalai kuwa ashe hasashena ya tabbata gaskiya, domin kuwa ashe tsohon ubangidansa ne, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso ya harzuƙa shi. Domin kuwa rahotanni sun tabbatar da cewa ya gana da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a gidan gwamnati.
Wata tambaya da ɗan jarida ya yi wa Ganduje ita ce: “Shin me za ka ce dangane da ziyarar Kwankwaso ga Tinubu?” Inda ya amsa cikin fushi, kamar zai kai naushi, yana cewa:
“Ai na san yana cikin Bila (Kwankwaso), sai dai Allah Ya so shi ba mu haɗu ba, domin lallai da mun haɗu, da na falla masa mari!”
Ni kuwa dariya ta cika mani ciki, na ce: Wai, ai kuwa da an ga teburin giwa. Yaya za mu ga Kwankwaso da Ganduje su
na asaƙala a gaban Tinubu? Wannan shi ne turnuƙu faɗan ibilisai, yaro bai gani ba balle ya raba!













