NAJERIYA A 65: MU SAKE DUBAWA
•••••••

A yau Najeriya ta cika shekara 65 da samun ‘yancin kai daga Turawan Birtaniya. Babu shakka lokaci ne da ya kamata al’umma, tun daga kan shugabanni da dukkan talakawa su duba, domin ganin inda aka kwana da kuma inda ya kamata a tashi.
A wannan tsawon lokaci, an samu hawa da sauka, an fuskanci wasu nasarori, kamar kuma yadda aka samu matsaloli manya da ƙanana. Amma mafi girma daga matsalolin da ke yi wa ƙasar nan barazana, ita ce matsalar tsaro. Babu shakka ya kamata gaba ɗaya a mayar da hankali wajen tunkarar wannan babbar matsala. Domin kuwa babu wani abu da zai yi tasiri a ƙasa, idan babu tsaro.
Haka kuma, lokacin ya yi da ya kamata a sake zama domin gyara tafiyar dimokuraɗiyya, madamar dai ana son ganin ci gaba. Ya kamata a zauna a yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar nan gyara na musamman, yadda za a samar da turba mai ɗorawa, musamman ganin cewa wannan tsari na Shugaba Mai Cikakken Iko, bai dace da Najeriya ba.
Haka kuma a sake duba tsarin iliminmu, wanda ya kamata a ce ya zuwa yanzu ya ta’allaƙa da koya wa ɗalibai hanyoyin sana’a da ƙere-kere, ba kawai yadda ake koya karatun-aku-kuturu ba. Ɗalibi ya shekara biyar a jami’a amma ya ce zai zura wa gwamnati ido ta sama masa aiki.
Haka ma batun harshen ƙasa, yana da matuƙar muhimmanci. Ya kamata ya zuwa yanzu a ce Najeriya tana da harshen ƙasa, ba Turanci ba. Mafi yawan ƙasashen duniya da suka ci gaba, da harshensu suke tafiyar da lamurran ƙasa.
Muna roƙon Allah ya ƙara wa ƙasarmu albarka. Ya ba mu lafiya da zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki.
_______________













