Shugaban Ƙasa, Ahmad Tinubu ya sauke Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Mista Godwin Emefiele, kamar yadda wata takarda da Jami’in Watsa Labarai a Fadar Shugaban Ƙasa, Mista Willie Bassey ya fitar.
An kuma buƙaci ya miƙa dukkan ragamar aikinsa ga jami’i mafi girma a Babban Bankin na CBN.
Wata majiya ta ce akwai yiwuwar a kama shi domin gudanar da binciken yadda ya gudanar da aikinsa.













