• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, September 20, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

KIRA NA MUSAMMAN GA JAMI’AN TSARO A MALUMFASHI

ƘORAFI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 3, 2024
in Gizago
1
KIRA NA MUSAMMAN GA JAMI’AN TSARO A MALUMFASHI

Garin Malumfashi

206
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

KIRA NA MUSAMMAN GA JAMI’AN TSARO A MALUMFASHI

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

SUNANTA UMMU-KHULSUM

SUNANTA UMMU-KHULSUM

September 13, 2026
HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

September 12, 2026
Garin Malumfashi

 

Ina son jawo hankalin JAMI’AN TSARO na garin Malumfashi Jihar Katsina, dangane da ƙorafin cewa wasu daga cikinsu, suna wuce makaɗi da rawa a yayin gudanar da aikinsu a cikin gari da kewaye.

A jiya Jumu’a, 27-01-1446 (Hijriyya), daidai da 02-08-2024 (Miladiyya) na samu kira tare da ƙorafi daga wani bawan Allah, daga Unguwar Gangarawa Malumfashi, inda ya sanar da ni wani abin takaici da ya faru a gidansa da na maƙwabtansa.

Kamar yadda ya ce, wani jami’in ɗan sanda ne, wanda yake ɗauke da bindiga ya shigo cikin gidansa da gudu, wai yana son kama wani yaro ne da yake cikin ‘yan zanga-zanga.

Ya ce ɗan sandan ya saka matansa da ‘ya’yansa da shi kansa cikin fargaba da tsoro, domin yadda jami’in yake ɗauke da bindiga kuma ya shigo gidan da tsananin gudu, babu ko sallama.

Ya ce da ya ƙalubalanci jami’in cewa ya fita daga gidansa, da ƙyar ya fita bayan ya ga yadda ransa ya ɓaci, tare da sanar da shi cewa bai kamata ya kutso gidansa ba tare da izini ba kuma ba tare da waranti daga alƙali ba.

Na samu bayanin cewa, ba gidan wannan bawan Allah kaɗai wasu jami’an ‘yan sanda tare da wasu ‘yan banga suka shiga ba. Ya ce a yayin da suke faturun, sun riƙa shiga gidajen mutane da nufin wai kama masu Zanga-zanga.

Bisa ga haka, ina kira ga shugabannin jami’an tsaro na Malumfashi, da su tsawata wa irin waɗannan jami’an tsaro, su gyara aikinsu domin su dace da kare haƙƙin shari’a. Lallai ya kamata a riƙa mutunta haƙƙin ‘yan Adam a yayin gudanar da aikin kare doka.

Batun gaskiya, shiga gidajen mutane ba tare da waranti na ƙa’ida ba, hakan wuce wuri ne kuma saɓa doka ne.

Allah Ya taimaki jami’an tsaron mu, Ya ba su nasarar magance dukkan matsalolin tsaro da muke fuskanta, Amin.

___________
Bashir Yahuza Malumfashi,
Babban Edita,
Mujallar Taskar Gizago (online)

Previous Post

NUJ Honors Gen. Buratai with Prestigious Award

Next Post

SHERIF ALMUHAJIR: JAMA’A YA KAMATA MU MUTUNTA JUNA

Related Posts

SUNANTA UMMU-KHULSUM
Gizago

SUNANTA UMMU-KHULSUM

September 13, 2026
HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1
Gizago

HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

September 12, 2026
Ayyukan Alheri Daga Gidan Amana
Gizago

Ayyukan Alheri Daga Gidan Amana

September 5, 2026
Next Post
SHERIF ALMUHAJIR: JAMA’A YA KAMATA MU MUTUNTA JUNA

SHERIF ALMUHAJIR: JAMA'A YA KAMATA MU MUTUNTA JUNA

Comments 1

  1. Yakubu Musa says:
    2 years ago

    Inda sunbari yaran sun tada rikici anyiwa mutane sata mezakayi kawai ankiraka kaikuma kayarda ko kuma dasu suka raunata yansandan fa to yaran dakake magana sunasone ayi rikici suyiwa mutane sata

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Tribute to Cultural Broadcaster: Muhammad Salissou Hamissou

Tribute to Cultural Broadcaster: Muhammad Salissou Hamissou

February 24, 2024
Abubakar Dalhatu Zurmi: Zahirin Ɗan Kasa Nagari Mai Kishin Ƙasa

Abubakar Dalhatu Zurmi: Zahirin Ɗan Kasa Nagari Mai Kishin Ƙasa

October 10, 2025
Ɗan Iyan Galadiman Katsina Emerges Chairman of Arewa Consultative Forum

Ɗan Iyan Galadiman Katsina Emerges Chairman of Arewa Consultative Forum

June 19, 2025
KARUWANCI GUBAR KASHE MATA

KARUWANCI GUBAR KASHE MATA

January 19, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso
  • JAGORA: Leader of the Masses
  • MALAM SULE LAMIDO: Jagoran Talakawa Ya Cika Shekaru 78

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

September 20, 2026
JAGORA: Leader of the Masses

JAGORA: Leader of the Masses

September 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.