• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, March 8, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Shanshani

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 20, 2023
in Shanshani
0
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

Kamun Ludayin Jemage

22
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

KAMUN LADUYIN JEMAGE (19-08-2023)

Daga Mukhtar Mudi Sipikin

Related posts

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

December 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023

~~~~~~~
Zaune nake jugudum ina ta karanta wasiƙar jaki, sai na ji “Ƙililin!” Saƙo ne ya sauka a cikin akwatin wayata. Na duba dai na ga ashe Malam Na Fagge ne ya turo mani shaguɓensa na mako, mai taken ‘Kamun Ludayin Jemage.” Ya ce, “Malam Shanshani, yau ma ga abin nan.” Ni kuwa na yi saurin karantawa. Jama’a, ku biyo ni mu karanta tare:
~~~~~~~

Hazbiya ta kalli tsuntsaye ta ce: “Ƴan uwana tsuntsaye, na yi mafarki cewa nan gaba kaɗan kifayen cikin ruwa za su fara tashi sama, suna shawagi a sararin samaniya. A cikin mafarkin kuma an nuna mun cewa bishiyoyin dajin nan za su fara tafiya. Ni dai na rikice, na kasa gane ma’anar wannan mafarkin da na yi.”

Kurciya ta yi murmushi, sannan ta ce: “Ke Hazbiya, ki gode Allah a mafarki kika ga wannan abubuwa masu rikita tunani, mu tsuntsayen dajin nan a zahiri muke ganin irin wannan lamura. Ko ba ki da labarin ma’aikatun da Jemage ya rarraba wa mataimakansa ba ko? Agwagwa, wadda duk duniya ta ƙware wajen iya ruwa, yanzu an tura ta kula da ma’aikatar kula da sheƙar tsuntsaye, Talotalo kuma da Ɗantsako wai su aka sanya a ma’aikatar tsaro ga ɓarnar Shaho…”

“Ni ba wanda ma ya fi ɗaure mun kai sai Kabarai, wanda aka naɗa a kan mai lura da walwalar tsuntsayen dajin nan. Kabarai fa, eanda ya yi ƙaurin suna wajen halayyar Yautai – Kaico!” Kanari ta tsalma baki.

Gado ya ce: “Wannan kamun ludayin na Jemage sai ka rasa gane ina ya dosa, kullum cikin birkita lamura yake, Allah Ya kyauta.” Tsuntsaye suka gama baki suka amsa da “Amin!”

Bainu ta kalli Alhudahuda ta ce: “Uban ‘yan boko!Me za ka ce a kan wannan lamari na Jemage? Amma don Allah ka yi magana mara sarƙaƙiya, yadda za mu fahimta. Yau dai a karo na farko, ka yi mana wannan alfarmar.”

Alhudahuda ya yi murmushi, sannan ya ce:
“Bainu kar ki bari zancen ‘yan duniya ya ruɗe ki. Ni ɗin nan ina ƙoƙari ƙwarai da gaske don ganin an fahimci zancena, kawai dai akasi ake samu. Yanzu dai tun da an buƙaci in ce wani abu a kan wannan abu da Jemage ya yi, to a yi mun afuwa, in ɗan karanto maku kaɗan daga cikin abin da na rubuta a ‘Diary’ na.”

Ya janyo wani ƙaton littafi duk ya yi ƙura, ya kaɗe shi, ya ɗauko tabarau ya ƙwama, sannan ya buɗe littafin, aka karkace aka fara karanto wa tsuntsaye abin da aka rubuta kamar haka:

“The Higgeledy-Piggidly Portfolio Appointments

The recent trend of appointing ministers by Jemage with little or no experience in their respective ministries has raised significant concerns about the effectiveness of governance. The term “heggedily-piggidly” aptly captures the chaotic and disorganized nature of these portfolio assignments, which undermine the very foundations of a well-functioning government.

The haphazard allocation of portfolios without regard for expertise has resulted in jumble approach to governance. It is alarming to witness ministers being placed in charge of crucial sectors where their knowledge and experience are sorely lacking. This approach not only handicaps the potential progress of these ministries but also casts doubts on the intentions behind such appointments…”

“Dakata haka! Mun fahimci matsayarka, mun gode, domin idan muka zuba maka ido sai a kai asuba ba ka tsaya ba. Mu ko bacci muke ji.” Tattabara ta katse shi.

Tsuntsaye suka yi sallama, kowa ya nufi sheƙarsa.

*Sai dai an samu rahoton balbelu sun fara lissafin yadda za su kasafta sulallan da Jemage ya ba su don a ragewa tsuntsaye raɗaɗin cire tallafin makamashin zirga-zirga.
~~~~~~~
Malam Mukhtar Mudi Sipikin, marubuci, sha’iri, ɗan siyasa kuma ɗan kasuwa ne. Ya rubuto wannan shaguɓe daga Kano.
~~~~~~~

Previous Post

GURƁATACCEN HATSI: An Ja Hankalin Hukumomin Jihar Katsina

Next Post

REGINA OGECHUKWU: Abubuwan Da Na Fahimta Daga Littafin Girl-Child Education in Biu Emirate

Related Posts

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU
Shanshani

SABON ZUMUNCI: KWANKWASO DA GANDUJE SUN YI SULHU

December 22, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE (26-08-2023 da 02-09-2023)

September 2, 2023
KAMUN LUDAYIN JEMAGE
Shanshani

KAMUN LUDAYIN JEMAGE

August 13, 2023
Next Post
REGINA OGECHUKWU: Abubuwan Da Na Fahimta Daga Littafin Girl-Child Education in Biu Emirate

REGINA OGECHUKWU: Abubuwan Da Na Fahimta Daga Littafin Girl-Child Education in Biu Emirate

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

INSECURITY IN MALUMFASHI: A CLARION CALL TO SERIOUS ACTION

INSECURITY IN MALUMFASHI: A CLARION CALL TO SERIOUS ACTION

March 6, 2025
Jan Hankali Ga Matasan Soshalmidiya

Jan Hankali Ga Matasan Soshalmidiya

July 11, 2023
NOMA YANKE TALAUCI: Ku Zo Mu Ziyarci Lungu Da Saƙon Gonar Ɗankano

NOMA YANKE TALAUCI: Ku Zo Mu Ziyarci Lungu Da Saƙon Gonar Ɗankano

August 22, 2023
KADA Honours Ambassador A. Y Shehu with Excellent Award

KADA Honours Ambassador A. Y Shehu with Excellent Award

September 1, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • RAMADAN KARIM: 19-1447
  • FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
  • RAMADAN KARIM: 18-1447

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

RAMADAN KARIM: 19-1447

RAMADAN KARIM: 19-1447

March 8, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.