DUNDUFAR SAITI
•••
Godiyar Allah na nanata,
Jallah Gwani Kai naka bauta,
Arrazaƙu ni’imto ruhina.
Manzo Muhammadu ne tutata,
Fitila mai haskaka hanyata,
Baban Fatima kai naka ƙauna.
Da uwa da uba duk kun kyauta,
A gare ni a yau kun alkinta,
Kun kyautata dukkan sashena.
‘Yan uwa na jini ga caffata,
A gare ni ku san kun cancanta,
Naku ne ni kullum na nuna.
Abokai na zumu ga shiftata,
Ku karanta don ku rabauta,
Mu guje wa dukka hiyana.
Duniya muke yau mun saba ta,
Wata rana mu mace komai rata,
Mu guje ta kar fa mu ƙuna.
Mu sani mun zo ne bauta,
Mu guje shirka don mu rabauta,
Mu gaje gidajen dukka aljanna.
Mu guje dukka ruɗin Shaiɗani,
Mai ingiza mu zuwa hairani,
Mu haɗe kai mu guje saɓani.
Ɗan uwa zo nan mu yi zance,
Mai inganci don fa mu tantance,
Shawarar kirki duk sai an zauna.
‘Yar uwa ke ma zo nan duba,
Kisan baƙi aikin gayya babba,
Ga zance mai ƙima tattauna.
A yau duniya ta lalace,
Mu ankare kar mu sakankance,
Hanyar kirki kar mu yi sauna.
Dakarun Dujjal sun yo kuwwa,
Karuwai, ‘yan daudu suna shewa,
Mu guje assha ya ku dangin juna.
Ƙofar fitina sun bubbuɗe ta,
Shoshalmidiya yau ta zama jita,
Maza da mata ana daddasa ɓarna.
An cire kunya wai su “wayewa,”
Malumanmu ana daɗa takawa,
Aikin fajirci jiddadun mummuna.
Aure sunna yau ya zama jari,
Sharholiya ake ita ce tsari,
Rayuwa ta birai dillalan ɓarna.
Mu sani ya ku dangina,
Duniya tai nisa mu tuna,
Mu zo mu riƙe babbar sunna.
Mu guje cinye amana, tozarci,
Mu daina gulma da zunɗe fajirci,
Annamimanci ciwo mu daina zina.
Mu aikata alheri shi ne hanya,
Sallah, Azumi, Zakka, Hajji sanya,
Imani ne farko sannan riƙe sunna.
Mu roƙi Allah domin dacewa,
Ya sauƙaƙa mana sauƙaƙawa,
Nasarar duniya da gobe zumuna.
Ya Allah amsa min addu’ata,
Kullum Ka ƙarfafi niyyata,
ALJANNA ta zamto ɗakina!
Mai ƙasida ya gama aiki nan,
Bashir Yahuza mai isharar nan,
Na Malumfashi garin gadona.
•••
© Bashir Yahuza Malumfashi
Asabar, 13-09-1445 (Hijriyya)
13-03-2024 (Miladiyya)
•••













