• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, July 10, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Wasanni

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

WASANNI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 9, 2026
in Wasanni
0
Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

A bana, za a fafata gumurzun leda ba tare da Najeriya ba

22
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

July 10, 2026
Lionel Messi: Tauraron Da Ya Sauya Tarihin Ƙwallon Ƙafa A Duniya

Lionel Messi: Tauraron Da Ya Sauya Tarihin Ƙwallon Ƙafa A Duniya

July 1, 2026

__________

Yayin da jibi Alhamis ake fara Gasar Kofin Kwallon Ƙafa Ta Duniya (FIFA 2026) a ƙasashen Amurka, Kanada da Mexico, ana sa ran za ta kasance ɗaya daga cikin manyan gasa mafi ƙayatarwa a tarihin ƙwallon ƙafa.

Kamar yadda Kamfanin Dillacin Labarai na Reuters ya ruwaito, wannan ne karo na farko da za a samu ƙasashe 48 da za su fafata a gasar, maimakon ƙasashe 32 da aka saba da su; lamarin da zai ba ƙarin ƙasashe damar nuna bajintarsu. Hakan zai sanya gasar ta ƙara zafi, armashi da kuma ɗaukar hankali, tun daga matakin rukuni har zuwa wasan ƙarshe.

Daga cikin fitattun ‘yan wasan da ake sa ran za su haskaka a gasar, akwai Kylian Mbappé, Erling Haaland, Jamal Musiala, Lionel Messi, Cristiano Ronaldo, da kuma Neymar. Duk da cewa wasu daga cikinsu sun manyanta amma har yanzu suna da ƙwarewa da gogewar da za su iya sauya sakamakon wasa a kowane lokaci.

Idan aka duba ƙasashen da ake ganin za su yi abin kirki a gasar, ƙasashen Turai suna kan gaba. Spain, France, England, Germany da Portugal suna cikin manyan waɗanda masana da masu hasashen sakamako ke ganin za su iya kai wa matakin ƙarshe. Haka kuma ba za a manta da Argentina da Brazil ba, domin suna da babbar ƙungiya, wacce ta goge a fafatawa a manyan gasa.

A bana, za a fafata gumurzun leda ba tare da Najeriya ba

Kafar talabijin ta CBS Sports ta ruwaito cewa, a nahiyar Afirka kuwa, ƙasar da mafi yawan masana ke hasashen za ta taɓuka abin kirki, ita ce Morocco. Bayan ta yi nasarar wasan kusa da na ƙarshe a gasar 2022, Morocco ta ci gaba da nuna bajinta a wasannin neman gurbin shiga gasar ta duniya kuma tana cikin ƙasashen Afirka da ake ganin za su iya sake girgiza manyan ƙasashe.

A rahoton BBC kuwa, masana sun ce baya ga Morocco, ana sa ran Senegal za ta yi ƙoƙari sosai, duk da ta samu kanta a cikin rukunin ƙasashe masu ƙwarewa. Ƙungiyar tana da gogaggun ‘yan wasa da suka saba buga manyan wasanni kuma za ta iya kai wa zagaye na gaba, idan ta yi amfani da damar da za ta samu.

Haka kuma ƙasar Egypt tana da kyakkyawar damar yin bajinta a gasar ta bana saboda kasancewar Mohamed Salah cikin tawagar, yayin da Ivory Coast ke da haziƙan matasan ‘yan ƙwallo masu iya ba da mamaki.

Wani abin da zai iya ba da mamaki a gasar, shi ne yadda ƙananan ƙasashe za su yi amfani da sabon tsarin gasar mai ƙungiyoyi 48. A tarihin kofin duniya, kusan kowace gasa tana samar da wata ƙasa da ba a yi tsammani ba, wadda take samun nasarar isa mataki mai nisa. Saboda haka, ba abin mamaki ba ne idan muka ga ƙasashe irin su Japan, Norway ko wasu daga Afirka suna girgiza manyan ƙasashe.

A taƙaice, idan za a yi hasashe, ƙasashen France, Spain, Brazil da Argentina su ne ke da damar lashe kofin gasar ta bana. A Afirka kuwa, Morocco ce take da mafi girman damar kai wa matakin kusa da na ƙarshe a gasar, yayin da Senegal da Egypt za su iya taka muhimmiyar rawa; idan suka samu kyakkyawar sa’a a wasanninsu na farko.

Idan hakan ta faru, akwai yiwuwar mu ga wata ƙasar Afirka ta sake kafa sabon tarihi a wannan gasa. A bana dai za a gurza leda, ba tare da Ƙungiyar Super Eagles ta Najeriya ba, domin kuwa “Giwar ta Afirka” ta kasa kai bantenta na zuwa gasar.

Previous Post

Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido

Next Post

Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

Related Posts

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana
Wasanni

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

July 10, 2026
Lionel Messi: Tauraron Da Ya Sauya Tarihin Ƙwallon Ƙafa A Duniya
Wasanni

Lionel Messi: Tauraron Da Ya Sauya Tarihin Ƙwallon Ƙafa A Duniya

July 1, 2026
FIFA World Cup 2026: Yau Akwai Gumurzu Tsakanin Brazil Da Morocco
Wasanni

FIFA World Cup 2026: Yau Akwai Gumurzu Tsakanin Brazil Da Morocco

June 13, 2026
Next Post
Inna Lillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

Inna Lillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un! Allah Ya Ji Ƙan Malam Lawal

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

An Kammala Jana’izar Shugaba Buhari Cikin Jimami Da Alhini

An Kammala Jana’izar Shugaba Buhari Cikin Jimami Da Alhini

July 16, 2025
AN DAKATAR DA MALAMIN MUSULUNCI DAGA YIN WA’AZI

AN DAKATAR DA MALAMIN MUSULUNCI DAGA YIN WA’AZI

November 19, 2024
KISAN MAWAƘI MOHBAD: Darasi Da Jan Hankali G Al’ummar Arewa

KISAN MAWAƘI MOHBAD: Darasi Da Jan Hankali G Al’ummar Arewa

September 22, 2023
Go Back to the Roots, Write in African Tongues – PAWA

Go Back to the Roots, Write in African Tongues – PAWA

March 18, 2024

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana
  • Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage
  • Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

Afirka Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya Na Bana

July 10, 2026
Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

July 9, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.