TSOKACINMU NA YAU (12)
Yau Laraba, 12-Ramadan-1446, Hijirar Manzon Allah (saw), wacce ta yi daidai da 12-Maris-2025, Miladiyya.
Ga tsokacinmu na yau:
“Ya ku ‘yan uwa, a yau tsokacinmu zai fuskanci jan hankali ne game da al’amuran siyasa. Abin fahimta dai shi ne, ita siyasa ra’ayi ce kuma zaɓi ne na mutum. Don haka a bi ta da tunani da hankali.
A siyasa, babu komai na dindindin – za ka iya shan inuwa ɗaya da masoyinka a yau, gobe kuma ka gan ka tare da maƙiyinka a inuwa ɗaya.
Babban saƙonmu na yau dai shi ne, mu kiyayi gaba ko ƙiyayya a siyasa.”
Allah sa mu dace, Amin.
Mu wuni lafiya.
Naku,
Bashir Yahuza Malumfashi,
Editan Mujallar Taskar Gizago.












