Daga Bashir Yahuza Malumfashi
Tare da sallama, ya ku masu bibiyar wannan shafi na Sinadarin Rayuwa, Assalamu alaikum. Bayan haka, yau kuma za mu ci gaba da yi wa juna tambihi game da maudu’in da muka faro a makon jiya, game da kishin ƙasa da kuma muhimmancinsa ga al’umma.
Kishin ƙasa ne ga mutum ya kasance mai ƙaunar jama’a, ba tare da nuna wariyar ƙabilanci, ɓangaranci ko addinanci ba. Kada ka ce za ka yi mu’amala ne kawai da ’yan ƙabilarka ko kuma ka ce ’yan ƙabilarka ne kaɗai mutanen kirki, don haka babu ruwanka da wasu. Idan ka yi haka, babu shakka ba ka nema wa ƙasarka alheri ba kuma ba ka zama mai kishinta ba.
A lokacin da ka ɗauki ’yan ƙabilarka kawai a matsayin mutane, ka banzatar da sauran jama’a, kawai domin su ba naka ba ne, to lallai akwai matsala. Na farko dai, kai kanka za ka gamu da matsala, domin kuwa al’ummar ƙasarka sun kasance ƙabilu daban-daban, masu yaruka daban-daban, masu al’adu daban-daban, kuma ya zama wajibi su yi rayuwa tare da wasu ƙabilun, tun da duk ’yan Najeriya ne. Wata rana, dole ne za ka nemi wata buƙata, wacce ɗan ƙabilarka ba zai biya maka ita ba. Idan haka ta kasance, to yaya za ka yi, tun da ba ka ɗauke su a bakin komai ba?
Idan mun duba da idon basira, duk wani addinin da ya amsa sunansa, ba ya son al’umma su nuna wariyar ƙabilanci. Babban burin kowane addinin ƙwarai shi ne, al’umma su kasance tsintsiya ɗaya, ta yadda za su amfani juna wajen zamantakewa da mu’amala. Hasali ma, Allah (SAW) Ya shaida mana cewa Ya halicci al’umma ne zuwa ƙabilu da jinsuna daban-daban, ba don komai ba sai domin su fahimci junansu.
Wannan yana nuna mana cewa, maimakon mu riƙa nuna ƙyama da wariya ga ƙabilun da ba namu ba, kamata ya yi mu fahimci juna, ta yadda za mu amfani juna kuma mu ci gajiyar juna.Wannan ne ma ya sanya na tuno da wani kalami da wani jigon al’umma, mai kishin ƙasa da al’ummarsa ya taɓa furtawa.
Ina maganar Gamji ɗan ƙwarai ne, wato marigayi Sardaunan Sakkwato, Alhaji Sa Ahmadu Bello. Kamar yadda aka ruwaito, an ce marigayi Dokta Nnamdi Azikiwe ne ya taɓa ce masa su mance da bambance-bambancensu…Shi kuwa Gamji sai ya ce masa ba haka za su yi ba, madamar suna son fahimtar juna.
Kamar yadda aka ruwaito, Sardauna ya ce wa Zik su zo su gane bambance-bambancensu sai su fahimci juna, su yi aiki tare alhali suna masu kiyaye haƙƙoƙin juna. Ya ce Zik Inyamuri ne, shi kuwa Bahaushe. Zik mutumin Kudu ne, shi kuwa ɗan Arewa. Zik Kirista ne, shi kuwa Musulmi. Ta haka za su haɗa hannu su yi wa ƙasa hidima.
Kuma wannan al’amari, ta kowane janibi muka duba shi, za mu gane tasirinsa, kasancewar kowa na buƙatar kowa. A yayin da Allah Ya hore wa wannan ƙabila wannan baiwa, Ya kuma hore wa waccan wata baiwar ta daban. Sai a haɗu tare, kowa ya baza kolin tasa baiwar domin amfanin juna. Wannan shi ne kishin ƙasa kuma da na al’umma.
Idan muka ɗauki mummunan halin nan na ɓangaranci kuwa, shi ma muninsa ɗaya da ƙabilanci. Madamar muna son mu kasance ’yan kishin ƙasa, masu son ganin al’umma ta samu ci gaba, dole ne mu rungumi juna, ba tare da la’akari da ɓangaren da junanmu suka fito ba.
Babban abin da a har kullum ya kamata mu riƙa kallo shi ne, ƙasa ɗaya ke gare mu, wacce ita ce mallakinmu. Ba mu da wata ƙasa da za mu iya kira tamu face ita. Ke nan da zarar Kudu ta bunƙasa, to Najeriya ce ta bunƙasa, haka ma Arewa.
(Za mu ci gaba)













