• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, June 13, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Sinadarin Rayuwa

Kishin Ƙasa Ne Tubalin Farko Na Gina Rayuwar Al’umma (2)

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 29, 2023
in Sinadarin Rayuwa
0
Kishin Ƙasa Ne Tubalin Farko Na Gina Rayuwar Al’umma (2)

© Bashir Yahuza Malumfashi

15
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Tare da sallama, ya ku masu bibiyar wannan shafi na Sinadarin Rayuwa, Assalamu alaikum. Bayan haka, yau kuma za mu ci gaba da yi wa juna tambihi game da maudu’in da muka faro a makon jiya, game da kishin ƙasa da kuma muhimmancinsa ga al’umma.

Related posts

Kada Ka Karaya Da Rayuwa

Kada Ka Karaya Da Rayuwa

November 30, 2025
Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

November 24, 2025

Kishin ƙasa ne ga mutum ya kasance mai ƙaunar jama’a, ba tare da nuna wariyar ƙabilanci, ɓangaranci ko addinanci ba. Kada ka ce za ka yi mu’amala ne kawai da ’yan ƙabilarka ko kuma ka ce ’yan ƙabilarka ne kaɗai mutanen kirki, don haka babu ruwanka da wasu. Idan ka yi haka, babu shakka ba ka nema wa ƙasarka alheri ba kuma ba ka zama mai kishinta ba.

A lokacin da ka ɗauki ’yan ƙabilarka kawai a matsayin mutane, ka banzatar da sauran jama’a, kawai domin su ba naka ba ne, to lallai akwai matsala. Na farko dai, kai kanka za ka gamu da matsala, domin kuwa al’ummar ƙasarka sun kasance ƙabilu daban-daban, masu yaruka daban-daban, masu al’adu daban-daban, kuma ya zama wajibi su yi rayuwa tare da wasu ƙabilun, tun da duk ’yan Najeriya ne. Wata rana, dole ne za ka nemi wata buƙata, wacce ɗan ƙabilarka ba zai biya maka ita ba. Idan haka ta kasance, to yaya za ka yi, tun da ba ka ɗauke su a bakin komai ba?

Idan mun duba da idon basira, duk wani addinin da ya amsa sunansa, ba ya son al’umma su nuna wariyar ƙabilanci. Babban burin kowane addinin ƙwarai shi ne, al’umma su kasance tsintsiya ɗaya, ta yadda za su amfani juna wajen zamantakewa da mu’amala. Hasali ma, Allah (SAW) Ya shaida mana cewa Ya halicci al’umma ne zuwa ƙabilu da jinsuna daban-daban, ba don komai ba sai domin su fahimci junansu.

Wannan yana nuna mana cewa, maimakon mu riƙa nuna ƙyama da wariya ga ƙabilun da ba namu ba, kamata ya yi mu fahimci juna, ta yadda za mu amfani juna kuma mu ci gajiyar juna.Wannan ne ma ya sanya na tuno da wani kalami da wani jigon al’umma, mai kishin ƙasa da al’ummarsa ya taɓa furtawa.

Ina maganar Gamji ɗan ƙwarai ne, wato marigayi Sardaunan Sakkwato, Alhaji Sa Ahmadu Bello. Kamar yadda aka ruwaito, an ce marigayi Dokta Nnamdi Azikiwe ne ya taɓa ce masa su mance da bambance-bambancensu…Shi kuwa Gamji sai ya ce masa ba haka za su yi ba, madamar suna son fahimtar juna.

Kamar yadda aka ruwaito, Sardauna ya ce wa Zik su zo su gane bambance-bambancensu sai su fahimci juna, su yi aiki tare alhali suna masu kiyaye haƙƙoƙin juna. Ya ce Zik Inyamuri ne, shi kuwa Bahaushe. Zik mutumin Kudu ne, shi kuwa ɗan Arewa. Zik Kirista ne, shi kuwa Musulmi. Ta haka za su haɗa hannu su yi wa ƙasa hidima.

Kuma wannan al’amari, ta kowane janibi muka duba shi, za mu gane tasirinsa, kasancewar kowa na buƙatar kowa. A yayin da Allah Ya hore wa wannan ƙabila wannan baiwa, Ya kuma hore wa waccan wata baiwar ta daban. Sai a haɗu tare, kowa ya baza kolin tasa baiwar domin amfanin juna. Wannan shi ne kishin ƙasa kuma da na al’umma.

Idan muka ɗauki mummunan halin nan na ɓangaranci kuwa, shi ma muninsa ɗaya da ƙabilanci. Madamar muna son mu kasance ’yan kishin ƙasa, masu son ganin al’umma ta samu ci gaba, dole ne mu rungumi juna, ba tare da la’akari da ɓangaren da junanmu suka fito ba.

Babban abin da a har kullum ya kamata mu riƙa kallo shi ne, ƙasa ɗaya ke gare mu, wacce ita ce mallakinmu. Ba mu da wata ƙasa da za mu iya kira tamu face ita. Ke nan da zarar Kudu ta bunƙasa, to Najeriya ce ta bunƙasa, haka ma Arewa.
(Za mu ci gaba)

Previous Post

Ɗalibi Ɗan Najeriya Ya Mutu A Yayin Faɗa A Amurka

Next Post

Rasheedah Tana Wa Al’umma Barka Da Sallah

Related Posts

Kada Ka Karaya Da Rayuwa
Sinadarin Rayuwa

Kada Ka Karaya Da Rayuwa

November 30, 2025
Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara
Sinadarin Rayuwa

Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

November 24, 2025
A Rayuwa: Alheri Danƙo Ne
Sinadarin Rayuwa

A Rayuwa: Alheri Danƙo Ne

November 11, 2025
Next Post
Rasheedah Tana Wa Al’umma Barka Da Sallah

Rasheedah Tana Wa Al'umma Barka Da Sallah

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Towards Nigeria 2027: Major Gladiators’ Prospects and Challenges

Towards Nigeria 2027: Major Gladiators’ Prospects and Challenges

March 27, 2025
KADA Honours Ambassador A. Y Shehu with Excellent Award

KADA Honours Ambassador A. Y Shehu with Excellent Award

September 1, 2024
Shugaba Tinubu Ya Sauke Shugabannin Rundunonin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Sauke Shugabannin Rundunonin Tsaro

June 19, 2023
General Buratai (A Poem)

General Buratai (A Poem)

April 26, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Yau Za A Fafata Tsakanin Canada Da Bosnia-Herzegovina
  • Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar
  • Kotu Ta Ayyana Hausawa Da Fulani Halastattun ‘Yan Ƙasa A Jihar Filato

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Yau Za A Fafata Tsakanin Canada Da Bosnia-Herzegovina

Yau Za A Fafata Tsakanin Canada Da Bosnia-Herzegovina

June 12, 2026
Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

Sojan Gona: An Kama Sojan Bogi Mai Muƙamin Manjo-Janar

June 12, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.