• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Tuesday, June 9, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Wasanni

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

WASANNI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
June 9, 2026
in Wasanni
0
Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

A bana, za a fafata gumurzun leda ba tare da Najeriya ba

6
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya

Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya

November 17, 2025

__________

Yayin da jibi Alhamis ake fara Gasar Kofin Kwallon Ƙafa Ta Duniya (FIFA 2026) a ƙasashen Amurka, Kanada da Mexico, ana sa ran za ta kasance ɗaya daga cikin manyan gasa mafi ƙayatarwa a tarihin ƙwallon ƙafa.

Kamar yadda Kamfanin Dillacin Labarai na Reuters ya ruwaito, wannan ne karo na farko da za a samu ƙasashe 48 da za su fafata a gasar, maimakon ƙasashe 32 da aka saba da su; lamarin da zai ba ƙarin ƙasashe damar nuna bajintarsu. Hakan zai sanya gasar ta ƙara zafi, armashi da kuma ɗaukar hankali, tun daga matakin rukuni har zuwa wasan ƙarshe.

Daga cikin fitattun ‘yan wasan da ake sa ran za su haskaka a gasar, akwai Kylian Mbappé, Erling Haaland, Jamal Musiala, Lionel Messi, Cristiano Ronaldo, da kuma Neymar. Duk da cewa wasu daga cikinsu sun manyanta amma har yanzu suna da ƙwarewa da gogewar da za su iya sauya sakamakon wasa a kowane lokaci.

Idan aka duba ƙasashen da ake ganin za su yi abin kirki a gasar, ƙasashen Turai suna kan gaba. Spain, France, England, Germany da Portugal suna cikin manyan waɗanda masana da masu hasashen sakamako ke ganin za su iya kai wa matakin ƙarshe. Haka kuma ba za a manta da Argentina da Brazil ba, domin suna da babbar ƙungiya, wacce ta goge a fafatawa a manyan gasa.

A bana, za a fafata gumurzun leda ba tare da Najeriya ba

Kafar talabijin ta CBS Sports ta ruwaito cewa, a nahiyar Afirka kuwa, ƙasar da mafi yawan masana ke hasashen za ta taɓuka abin kirki, ita ce Morocco. Bayan ta yi nasarar wasan kusa da na ƙarshe a gasar 2022, Morocco ta ci gaba da nuna bajinta a wasannin neman gurbin shiga gasar ta duniya kuma tana cikin ƙasashen Afirka da ake ganin za su iya sake girgiza manyan ƙasashe.

A rahoton BBC kuwa, masana sun ce baya ga Morocco, ana sa ran Senegal za ta yi ƙoƙari sosai, duk da ta samu kanta a cikin rukunin ƙasashe masu ƙwarewa. Ƙungiyar tana da gogaggun ‘yan wasa da suka saba buga manyan wasanni kuma za ta iya kai wa zagaye na gaba, idan ta yi amfani da damar da za ta samu.

Haka kuma ƙasar Egypt tana da kyakkyawar damar yin bajinta a gasar ta bana saboda kasancewar Mohamed Salah cikin tawagar, yayin da Ivory Coast ke da haziƙan matasan ‘yan ƙwallo masu iya ba da mamaki.

Wani abin da zai iya ba da mamaki a gasar, shi ne yadda ƙananan ƙasashe za su yi amfani da sabon tsarin gasar mai ƙungiyoyi 48. A tarihin kofin duniya, kusan kowace gasa tana samar da wata ƙasa da ba a yi tsammani ba, wadda take samun nasarar isa mataki mai nisa. Saboda haka, ba abin mamaki ba ne idan muka ga ƙasashe irin su Japan, Norway ko wasu daga Afirka suna girgiza manyan ƙasashe.

A taƙaice, idan za a yi hasashe, ƙasashen France, Spain, Brazil da Argentina su ne ke da damar lashe kofin gasar ta bana. A Afirka kuwa, Morocco ce take da mafi girman damar kai wa matakin kusa da na ƙarshe a gasar, yayin da Senegal da Egypt za su iya taka muhimmiyar rawa; idan suka samu kyakkyawar sa’a a wasanninsu na farko.

Idan hakan ta faru, akwai yiwuwar mu ga wata ƙasar Afirka ta sake kafa sabon tarihi a wannan gasa. A bana dai za a gurza leda, ba tare da Ƙungiyar Super Eagles ta Najeriya ba, domin kuwa “Giwar ta Afirka” ta kasa kai bantenta na zuwa gasar.

Previous Post

Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido

Related Posts

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
Wasanni

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya
Wasanni

Matsalolin Da Suka Daƙile Super Eagles Daga Gasar Kofin Duniya

November 17, 2025
PSG DA ARSENAL: ZARATAN ‘YAN WASAN DA ZA SU BA DA MAMAKI
Wasanni

PSG DA ARSENAL: ZARATAN ‘YAN WASAN DA ZA SU BA DA MAMAKI

April 29, 2025

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

TSOKACINMU NA YAU (05)

TSOKACINMU NA YAU (05)

March 5, 2025
Malaman Zamani: Wa’azi Ko Gyaran Gangar Auzinawa?

Malaman Zamani: Wa’azi Ko Gyaran Gangar Auzinawa?

September 15, 2023
EFCC Ta Kai Farmaki Jihar Katsina

EFCC Ta Kai Farmaki Jihar Katsina

June 9, 2023
Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

June 9, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa
  • Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido
  • Illolin Yaɗa Hotuna Da Bidiyon Aika-Aikar ‘Yan Ta’addar Daji

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

Gasar Kofin Ƙwallon Ƙafa Ta Duniya: Jibi Ne Fa

June 9, 2026
Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido

Sharhin Littafin Tarihin Rayuwar Sule Lamido

June 8, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.