BAKIN JAƁA (7)
(Labarin Cin Amana)
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
Bayan mutuwar jaririn Jummalo, an sha marƙabu da jeka-ka-dawo tsakanin hukumomi, har zuwa dai daga ƙarshe aka bar maganar ta bi shanun sarki. Ma’ana dai babu wani hukunci da ya biyo bayan wannan aika-aika da ta aikata, domin a cewar su, babu wata ƙwakkwarar shaida da ta tabbatar da cewa ita ta halaka jaririn.
Ta faru ta ƙare, wai an yi wa mai dami ɗaya sata. Mahaifin Jummalo yana ji kuma yana gani, amma ba a son ransa ba, ɗiyarsa ta tsunduma kacokan cikin kasuwar jawarci. Ga ta dai yarinya ɗanya shar (sakin wawa), ba ciki kuma babu goyo. A kullum idan gari ya waye ba ta da aiki sai kwanciya, sai kallace-kallacen finafinai. Idan ta gaji da kallo, sai ta kunna sauti a akwatin MP3 ta ƙure iya ƙararsa, ta bi lafiyar katita. Babu ruwanta da salla balle salati. Kuma babu abin da ya shalli kakarta da innarta!
Hikima Drama Joint gida ne da ya shahara a garin su Jummalo. Matattara ce ta matasa maza da mata, da ma duk wanda ke son shaƙatawa. Sukan fara wasan kaɗe-kaɗe da raye-raye da misalin ƙarfe biyar na yammacin kowace rana, sannan kuma su ƙarƙare da wasan kwaikwayo na daɓe. Haka kuma da dare sukan ɗora daga inda suka tsaya, daga nan har tsakiyar zuwa dare. Jummalo ta maida gidan nan tamkar gidanta na biyu. Ko runhu mutum ya riƙo, madamar yana nemanta, to da ya zo gidan diramar nan zai same ta.
A kullum ta kasa samun nutsuwa, ta kuma daina sauraron shawarar iyayenta, musamman ma mahaifinta, wanda a kullum yake roƙonta ta gyara halinta amma kamar yana saran ruwa.
A cikin ‘yan wasan gidan Drama Hikima Joint, akwai wata yarinya da jininta ya haɗu da na Jummalo, inda suka zama ƙawaye. Kusan a kullum suna tare. Yarinya ce kyakkyawa, wacce kuma daga Kano take. Tana daga cikin jami’an da ke gudanar da shirye-shiryen wasan kwaikwayo da raye-raye a wannan gidan dirama. Sunanta Hajara amma an fi saninta da laƙanin Takano. Tana da hazaƙa sosai, domin ita ce ma jagaba a fannin rubuta wasannin kwaikwayo da ba da umurmi ga ‘yan wasa a gidan.
Wata rana da Jummalo ta je gidan dirama, sai ta samu wuri ta zauna ta yi jugum. Abin duniya duk ya taru ya caɓe mata. A daidai wannan lokaci ne ta yi ta tunani, tana tariyar yadda rayuwarta ta kasance. A yayin da take cikin nazari da tunani, sai ta ankara da wasu ‘yan mata su biyu, suna zaune a can gefe guda suna zuƙar sigari, suna ta annashuwa suna ƙyalkyata dariya, tamkar babu wata matsala da ke damun su a rayuwa.
A cikin wannan yanayi ne ƙawarta Takano ta zo ta same ta. Sai da ta ɗauki tsawon lokaci tana tsaye amma Jummalo ba ta san ta zo ba, domin kuwa idanunta suna kafe ga ‘yan matan nan da suke shan sigari, a yayin da ta lula cikin tunani.
“Juma, me ya faru ne?” Takano ce ta jefa mata tambaya da murya mai ƙarfi, a lokaci guda kuma ta muskuta, ta zauna kusa da ita.
“Kash, har kin ba ni tsoro,” in ji ta. Babu abin da ya faru. Kawai ina ta nazarin rayuwa ce, sai hankalina ya kai ga ‘yan matan can biyu. Na ga suna ta jin daɗinsu.
“Ke dai ki bi a hankali da rayuwar nan, kada ki je ki zautu. Ba ki san cewa yawan tunani yana kawo damuwa ba? Ita kuma damuwa idan ta yi yawa, takan sa mutum ya susuce. Ki tashi mu je mu ɗan sha Soɓo.”
Bayan sun isa wajen mai shago da ke cikin harabar gidan wasan, sun sayi abin sha, sai suka samu wani benci suka zauna. A nan ne Takano ta tsegunta wa Jummalo labarin ‘yan matan nan biyu da ta gani suna hira. Ta shaida mata cewa ai ƙawaye ne kuma masoyan juna. Ta shaida mata cewa ana zarginsu ma da cewa sun ɗaura auren jinsi a junansu, a asirce.
“Kuma gaskiya, mu ma ya kamata mu natsu, mu duba rayuwarmu domin gaba,” in ji Takano.
“Kamar yaya cewa mu duba rayuwarmu? Ban gane ba.” Jummalo ta faɗi haka, a yayin da ta juyo da fuskarta ta kalli ƙawarta kai tsaye, cikin mamaki.
“Abin da nake nufi shi ne,” a cewar Takano. “Kin ga a labarin da kika gaya mani, kin taɓa aure har kin haihu. Ni kuwa ban ko taɓa aure ba amma dukkanmu mun fitsare ƙafafunmu. Ni na baro iyayena a Kano, na zo nan na tare ina bariki. Ke kuwa a gaban naki iyayen kike shuka bariki. Ba ki ganin idan muka ci gaba a haka, rayuwarmu za ta lalace gaba ɗaya?”
“Ina jin ki. To me kike so mu yi yanzu?” Jummalo ta ƙara natsuwa, ta tsotsi Soɓo, a yayin da ta zura wa Takano idanunta dara-dara kamar na autan ƙururu.
“Abin da nake nufi shi ne, mu duba rayuwarmu, mu yi tunanin abin da zai fisshe mu. Misali, ni kin ga na gama digiri, don haka ya kamata in samu aiki mai kyau, kuma in samu mijin aure maimakon wannan zaman da nake yi a gidan dirama. Duk da cewa ina samun kuɗi sosai amma babu mutunci, domin kowa kallon ‘yar iska yake mani.
“Ke kuma Juma, me zai hana ki koma makaranta ki gyara jarabawarki ta WAEC, sannan ki shiga babbar makaranta? Kin ga ke yarinya ce, kina da sauran chance a gaba. Kin san fa wannan zamani ne na ilimi, duk wanda ya zauna da jahilci tam…”
Jummalo ta yi tunani sosai, ta kuma ji kamar wannan shawara ce ta gaskiya. Bayan wasu watanni, sai ta sake rubuta jarabawarta ta WAEC kuma ta yi nasara sosai. Kodayake ba ita ta rubuta jarabawar da kanta ba. Takano ce ta shirya da malamai, suka ba da cin hanci. Shi ne aka amince ta yi ɓadda-bami, ta shiga zauren jarabawar a madadin Jummalo.
(Za Mu Ci Gaba)
_______________













