• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, May 11, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

Gidauniyar Bukar Usman Ta Tallafa Wa Hausawan Togo Da Littattafan Hausa

Muhammad Abu Hidaya by Muhammad Abu Hidaya
August 2, 2023
in Adabi
0
Gidauniyar Bukar Usman Ta Tallafa Wa Hausawan Togo Da Littattafan Hausa
70
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Gidauniyar Bukar Usman Ta Tallafa Wa Hausawan Togo Da Littattafan Hausa

Gidauniyar Bukar Usman ta tallafa wa al’ummar Hausawan ƙasar Togo gudunmawar littattafan Hausa, domin

Related posts

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
Wasu daga al’ummar Hausawan Togo
Muhammad Abu Hidaya, yana jawabi ga Hausawan Togo

inganta koyarwa a sabuwar makarantar koyar da harshen Hausa da aka buɗe, domin Ilimantar da al’ummar Hausawan ta ƙasar Togo.

Wannan ya biyo bayan ci gaba da yi wa harshen Hausa da al’adunsa hidima, inda aka samar da makarantar Hausa ta farko a ƙasar Togo, wadda Hausawan ƙasar suka assasa, ƙarƙashin ƙungiyar Hausawa ta Association Tarayya Togo da haɗin gwiwar gamayyar ƙungiyoyin Hausawa na ƙasashen Afrika mai suna Gidauniyar Zumunci.

Ranar 31/7/2023 aka buɗe wannan makarantar Hausa ta farko a ƙasar Togo da ɗalibai 15, ƙarƙashin kulawa da koyarwar Malam Rabi’u Muhammad Abu Hidaya, wanda shi ne shugaban Tsangayar Adabin HAUSA, haka kuma Mataimakin Shugaban Gamayyar Ƙungiyoyin Haɗaka na Harshen Hausa (GIZU). Har wa yau shi ne malamin da ya taso daga Nigeria zuwa ƙasar Togo domin bayar da horo ga ɗaliban da za su yi nazarin harshen Hausa a makarantar Hausa ta farko a Togo.

Hausawa a ƙasar Togo sun daɗe, domin kuwa sun shafe kimanin shekaru ɗari biyar (500), a cewar Shugaban Ƙungiyar Tarayya Togo, mai suna Alhaji Sulaiman Yahaya (Bala), kuma hukumar ƙasar Togo ta sanya su cikin ‘yan asalin ƙasar, masu aiki a dukkan sassan madafun iko na gwamnati. Saboda nisan lokaci, harshe da al’adun sun soma jin jiki, wannan ne dalilin da ya sa suka yunƙura aka assasa wannan makaranta don ci gaban harshen Hausa a matakin ilimi.

Ana fata wannan yunƙuri zai ci gaba da samun tagomashi daga jami’o’i da masu ruwa da tsaki kan ci gaban harshen Hausa a duniya.

Taron dai ya sami halartar dattawa da manyan jami’an gwamnatin ƙasar tare da wakilcin gungun sarakunan ƙasar Togo.

Previous Post

An Yi Gangamin Addu’o’in Godiya Ga Allah A Katsina

Next Post

TAURARON GIZAGAWA: NURA ADAMU AHMED

Related Posts

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
Adabi

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza
Adabi

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)
Adabi

FITILAR MATASA – Zannan Galadima (3)

March 7, 2026
Next Post
TAURARON GIZAGAWA: NURA ADAMU AHMED

TAURARON GIZAGAWA: NURA ADAMU AHMED

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

April 15, 2024
Limamin Kirista Da Mabiyansa Dubu 100 Sun Musulunta

Limamin Kirista Da Mabiyansa Dubu 100 Sun Musulunta

July 3, 2023
General Buratai (A Poem)

General Buratai (A Poem)

April 26, 2026
A Daina Rufa-Rafa Ga Matsalar Ruwa A Sakkwato

A Daina Rufa-Rafa Ga Matsalar Ruwa A Sakkwato

June 7, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi
  • Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi
  • Farewell Ashaka

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

Asibitoci A Najeriya Ba Su Da Bambanci Da Turakun Dabbobi

May 9, 2026
Yan ta’addan Daji Kafirai Ne  – Sarkin Musulmi

Yan ta’addan Daji Kafirai Ne – Sarkin Musulmi

May 8, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.