Gidauniyar Bukar Usman Ta Tallafa Wa Hausawan Togo Da Littattafan Hausa
Gidauniyar Bukar Usman ta tallafa wa al’ummar Hausawan ƙasar Togo gudunmawar littattafan Hausa, domin
inganta koyarwa a sabuwar makarantar koyar da harshen Hausa da aka buɗe, domin Ilimantar da al’ummar Hausawan ta ƙasar Togo.
Wannan ya biyo bayan ci gaba da yi wa harshen Hausa da al’adunsa hidima, inda aka samar da makarantar Hausa ta farko a ƙasar Togo, wadda Hausawan ƙasar suka assasa, ƙarƙashin ƙungiyar Hausawa ta Association Tarayya Togo da haɗin gwiwar gamayyar ƙungiyoyin Hausawa na ƙasashen Afrika mai suna Gidauniyar Zumunci.
Ranar 31/7/2023 aka buɗe wannan makarantar Hausa ta farko a ƙasar Togo da ɗalibai 15, ƙarƙashin kulawa da koyarwar Malam Rabi’u Muhammad Abu Hidaya, wanda shi ne shugaban Tsangayar Adabin HAUSA, haka kuma Mataimakin Shugaban Gamayyar Ƙungiyoyin Haɗaka na Harshen Hausa (GIZU). Har wa yau shi ne malamin da ya taso daga Nigeria zuwa ƙasar Togo domin bayar da horo ga ɗaliban da za su yi nazarin harshen Hausa a makarantar Hausa ta farko a Togo.
Hausawa a ƙasar Togo sun daɗe, domin kuwa sun shafe kimanin shekaru ɗari biyar (500), a cewar Shugaban Ƙungiyar Tarayya Togo, mai suna Alhaji Sulaiman Yahaya (Bala), kuma hukumar ƙasar Togo ta sanya su cikin ‘yan asalin ƙasar, masu aiki a dukkan sassan madafun iko na gwamnati. Saboda nisan lokaci, harshe da al’adun sun soma jin jiki, wannan ne dalilin da ya sa suka yunƙura aka assasa wannan makaranta don ci gaban harshen Hausa a matakin ilimi.
Ana fata wannan yunƙuri zai ci gaba da samun tagomashi daga jami’o’i da masu ruwa da tsaki kan ci gaban harshen Hausa a duniya.
Taron dai ya sami halartar dattawa da manyan jami’an gwamnatin ƙasar tare da wakilcin gungun sarakunan ƙasar Togo.