• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Monday, August 24, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Siyasa

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

DIKKON KATSINAWA

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 24, 2026
in Siyasa
0
Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

Dikkon Katsinawa (10)

3
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

Daga Bashir Yahuza Malumfashi
__________
A makon da ya gabata, wanda ya faro daga ranar Litinin 17 zuwa 23 ga Agusta, 2026, an gudanar da al’amura masu yawan gaske a Jihar Katsina, musamman ma ayyukan da suka danganci bunƙasa rayuwar al’ummar jiha, a ƙarƙashin jagorancin mai girma Gwamna Hadimin Talakawa, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, PhD, CON.

Related posts

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

July 24, 2026
Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

July 8, 2026

A makon da ya gabata ne, a ranar Juma’a, 21 ga Agusta, 2026, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Ph.D, CON, ya ƙaddamar da shugabannin Ƙungiyar APC Zalla, na ƙananan hukumomi 34 da mazabu 361 da suke a faɗin jihar.

Ƙungiyar, wadda Sadaukin Kankia, Dakta Bala Nuhu Kankia ya kafa kuma yake jagoranta, an ƙaddamar da ita ne a filin taro na People’s Square da ke Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

Da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Dikko Radda ya bayyana cewa a yanzu al’umma ba sa kallon alƙawuran da ake yi musu kawai, illa ayyukan da gwamnati ta gudanar a zahiri. Ya ce ayyukan da gwamnati ta aiwatar a faɗin jihar a bayyane suke kuma al’umma za su iya tantance su tare da yin hukunci a lokacin zaɓe.

Gwamna Dikko Umaru Raɗda a Musawa, yayin taron raba tallafi

Wasu daga cikin manyan da suka halarci taron, sun haɗa da tsohon Ministan Gidaje a Gwamnatin Tarayya, Arch. Ahmed Musa Dangiwa da Shugaban Jam’iyyar APC na Jihar Katsina, Hon. Bishir Gambo Saulawa da manyan ‘yan siyasa, kwamishinoni, masu ba Gwamna shawara, shugabannin jam’iyya, matasa, maza da mata da sauran al’umma daga sassa daban-daban na Jihar Katsina.

Haka kuma, duk dai a ranar ta Juma’a, 21 ga Agusta, 2026, Gwamna Malam Dikko Umaru Radda ya gana da masu ruwa da tsaki na Ƙaramar Hukumar Ingawa, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar, Hon. Abubakar Idris 02.

Waɗanda suka yi jawabi a yayin taron, sun haɗa da Shugaban Ƙaramar Hukumar Ingawa, Hon. Abubakar Idris 02 da Ubandoman Katsina, Hakimin ‘Yandoma, Alhaji Muntari Dambo da Ɗan Majalisar Jiha mai wakiltar Ingawa, Hon. Abubakar Sulaiman Tunas da Shugaban Masu Ruwa da Tsaki na Karamar Hukumar, Engr. Mustapha Mahmud Kanti. Dukkansu sun gabatar da godiya ga Gwamnan bisa ayyukan raya ƙasa da gwamnatin jihar ta gudanar a Karamar Hukumar Ingawa, tare da nuna cikakken goyon baya ga Gwamna da Jam’iyyar APC a zaɓukan da ke tafe.

A nasa jawabin, Gwamna Radda ya gode wa al’ummar Karamar Hukumar Ingawa, bisa goyon baya, haɗin kai da amincewar da suke ba gwamnatinsa. Ya kuma bayyana farin cikinsa bisa yadda ya ga masu ruwa da tsaki na ƙaramar hukumar suka haɗa kai tare da fahimtar juna a harkokin siyasa.

Malam Dikko a yayin taron bunƙasa al’ummar Jihar Katsina

Taron ya samu halartar PPS na Gwamnan, Hon. Abdullahi Aliyu Turaji; Kwamishinan Ayyuka da Sufuri, Engr. Sani Magaji Ingawa; Kwamishinan Wasanni da Matasa, Hon. Surajo Yazeed Abukur; Hon. Bala Sani Yaya; Hon. Labaran Magaji; Hon. Danlami Ingawa; Mai Martaba Sarkin Fulani Dambo, Alhaji Tukur Sulaiman Dambo; Hon. Akilu Mamman Yandoma; Dr. Bilyaminu Sulaiman; Shugaban Jam’iyyar APC na Karamar Hukumar, Hon. Yahya Champion, Kansiloli, ‘yan siyasa, mata, matasa da sauran masu ruwa da tsaki na Karamar Hukumar Ingawa.

A ranar Asabar, 22 ga Agusta, 2026, Gwamna Malam Dikko Umaru Radda ya ƙaddamar da rabon muhimman kayayyakin aiki da magunguna ga cibiyoyin kiwon lafiya daban-daban a faɗin jihar.

Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Katsina ce ta jagoranci shirin ta hannun Hukumar Kula da Magunguna da Kayayyakin Lafiya ta Jihar (DMSA), tare da tallafin Ƙungiyar Baitulmaal da shirin State-Wide Approach Programme (SWAP).

Gwamnan ya kuma umarci hukumomin lafiya da su tabbatar da adalci da gaskiya wajen rabawa, tare da tabbatar da an yi yadda ya kamata wajen amfani da kayayyakin da kuma kula da kayan aikin, domin su daɗe suna aiki yadda ya kamata.

Mahalarta taron sun haɗa da Mataimakin Gwamna, Malam Faruk Lawal Jobe da Hon. Abdullahi Aliyu Turaji, Kwamishinoni da sauran Jami’an Gwamnati.

Sai kuma a jiya Lahadi, 23 ga Agusta, 2026, inda Gwamna Malam Dikko Umaru Radda, ya ƙaddamar da rabon tallafin abinci, kuɗaɗe da sauran kayan agaji ga al’ummar Ƙaramar Hukumar Musawa, waɗanda hare-haren ‘yan ta’adda ya shafa.

Tallafin ya samu ne sakamakon haɗin gwiwar shugabannin siyasa da masu ruwa da tsaki na ƙaramar hukumar, musamman Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar yankin, Hon. Abdullahi Aliyu (Dujiman Katsina). Sun tanadar da kayayyakin ne, domin tallafa wa al’ummar yankin tare da rage musu raɗaɗin halin da suke ciki.

A yayin ƙaddamar da tallafin, an raba buhunan shinkafa 1,500 da buhunan taki 200, yayin da Hon. Abdullahi Aliyu Ahmad (Dujiman Katsina), ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 30 domin tallafa wa al’ummomin da lamarin tsaro ya shafa, ya kuma ba da Babura 109, ga masu gari, da sauran mutanen da suka hidimta masa a siyasa.

Sauran waɗanda suka ba da gudunmuwar akwai Muhammad Abu Ibrahim, Ministar Al’adu, Fasaha da Tattalin Arziki, Hon. Hannatu Musa Musawa (Naira miliyan 10), Alhaji Muttaqah Badaru (Naira miliyan 5), Hajiya Zainab Musa Musawa (Naira miliyan 5), Nura Tela (Naira miliyan 5) da sauran shugabannin siyasa da ‘yan asalin yankin.

Da yake jawabi, Gwamna Radda ya yaba da wannan kyakkyawan yunƙuri na ‘ya’an Musawa da Matazu, yana mai bayyana tallafin a matsayin wata muhimmiyar gudunmawa wajen rage wa al’ummar da suka fuskanci hare-haren ta’addanci raɗaɗin halin da suke ciki.

Waɗannan su ne kaɗan daga cikin muhimman al’amuran da suka wakana a Jihar Katsina a makon da ya gabata. Sai kuma ƙarshen wannan makon, idan Allah ya kai mu, za mu sake kawo maku sabon shiri. A huta lafiya.
__________

Previous Post

Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon

Related Posts

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya
Siyasa

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

July 24, 2026
Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti
Siyasa

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

July 8, 2026
Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya
Siyasa

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

June 17, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Jigawa State Government is Proactive on Walida’s Case – Hamisu Mohammed Gumel

Jigawa State Government is Proactive on Walida’s Case – Hamisu Mohammed Gumel

February 25, 2026
Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

Aiki Ya Fi Surutu: Muhimmin Darasi Ga Duk Mai Neman Nasara

November 24, 2025
SAKAMAKON FARKO NA GASAR RUBUTUN HAUSA TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

SAKAMAKON FARKO NA GASAR RUBUTUN HAUSA TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 1, 2025
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)
  • Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon
  • Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

Katsina A Makon Jiya (17-23-08-2026)

August 24, 2026
Bankwana Da Jigon Adabi: Ta’aziyyar Farfesa Bello Sa’idu

Professor Bello Sa’idu: The Demise of Literary Icon

August 23, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.