Daga Baba Bala Katsina
Gwamnatin Tinubu: Tallafin ₦8000 Ba Zai Yi Tasiri Ba!
Ba wani tsari da aka fito da shi wanda za ya maye gurbin raɗaɗin cire tallafin man fetur a Nigeria.
Yanzu ka duba wannan Naira dubu takwas da suka ce za su ba gidaje masu fama da matsin talauci mai yaɗo.
Ka lissafa ka gani: A garinku kaɗai akwai gidaje fiye da dubu 500 da ke cikin raɗaɗin talauci mai yaɗo, waɗanda idan aka ba su Naira dubu 8 ɗin nan duk wata, za ta rage masu raɗaɗin talauci. Sai dai kash, ko gida dubu ɗaya ba za su samu wannan tallafin ba, koda kuwa za a raba shi fisabilillahi, ba tare da cuwa-cuwa ba.
Kafin a cire tallafi, dukkan gidajen nan suna zuwa kasuwa suna sayen kaya da ƙyar, yanzu an cire tallafin fetur, duka mutanen gari rayuwarsu ta ƙara tsada, kuma hanyoyin neman abinci na mutanen da suke cen ƙasa sun ƙara wahala.
Amma yanzu ga shi da wahala fiye da gida 1000 su samu tallafin. To ta ina za a maye gurbin Za a dai ƙara yawan talakawa ne kawai.
Har yanzu kuma fa kar ku manta, masu mulki ba a cire masu TALLAFI ba, kuma har yanzu suna maganar a ƙara masu kuɗin albashi da alawus-alawus.
Ka ga rayuwarsu da ta mu za ta ƙara bambanta ke nan ƙwarai, inda za su iya yin rayuwa mai kyau. Sauran mutane kuma cutar Maleriya ta riƙa kashe su saboda ba su iya sayen magani.













