TSAKANIN MALAM PANTAMI DA HASSADAR MALAMAI
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Ashe haka malamai suke da tsananin hassada ga junansu? Babu shakka na yadda da cewa tabbas hassada da ƙyashin juna sun yi katutu a zukatan wasu malaman addini.
A kwanan nan ne na ƙara tabbatar da haka, musamman bisa la’akari da na yi, yadda a Jihar Gombe wasu rukunnan malaman addinin Musulunci suka yi ta kumfar baki tare da tada jijiyar wuya ga ɗan uwansu, tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami.
Abin mamaki ne yadda ɗaya daga cikinsu, ba kunya ba tsoron Allah, ya fito a bainannasi yana adawa da Sheikh Pantami. Yana faɗin cewa wai idan Allah ya kai mu 2027 wai “su malamai” a Jihar Gombe, ba za su goyi bayan Malam ya tsaya takarar Gwamna ba.
Abin mamaki, wai kare da tallar tsire. Ko kuma mu ce abin dariya, wai yara sun tsinci haƙori.
Kun san inda abin mamakin yake? Wai fa malami ne yake faɗin haka ga malami ɗan uwansa. Shin idan malamin addini bai goyi bayan ɗan uwansa mai nagarta kamar Sheikh Pantami ba, to wa zai goya wa baya? Jahili, ɗan duniya ke nan zai zaɓa? Kun ga ke nan, hassada da ƙyashi ne suka yi tasiri a nan!
Abin dariyar kuma shi ne, gurgun dalilin da malamin ya kawo, a matsayin hujjarsa ta rashin amincewa da Pantami. Abin da ya sanya na ce dililinsa gurgu ne, shi ne, wai a lokacin da Sheikh yake Minista, wai ba ya ɗaga kiran wayarsu. Wai kuma bai taimaki malaman Jihar Gombe ba da dukiya.
Ni kuwa na ce assha! Wai malami ne yake faɗin wannan mummunar magana, kamar wanda bai taɓa sanin Allah ba, balle amanarsa. Shin shi malamin nan bai san cewa dukiyar gwamnati ta al’umma ba ce? Yana son Malam ya ɗebi dukiyar al’umma ya raba masu? Shin bai san akwai ranar hisabi ba? Ke nan yana nufin wanda za su zaɓa ya zama Gwamna a Jihar Gombe, shi ne wanda zai buɗe masu bakin baitulmali su ɗebi dukiyar da suke so, ba wanda zai yi wa al’umma mulki da adalci ba?
Gaskiya an yi walƙiya mun ga idon kowa. Idan ba hassada ba, ai malamai, musamman ma a Jihar Gombe, kamata ya yi su yi murna da alfaharin yadda ɗan uwansu Malami ya riƙe babban muƙami a Gwamnatin Tarayya, kuma ya samu yabo na riƙe amana. Ko kuwa suna nufin ba su ga yadda Pantami ya samu shaida daga sassan duniya ba, yadda ya tafiyar da aikinsa na Ministan Sadarwa?
A batun gaskiya, muddin Farfesa Pantami ya fito takarar Gwamna a Jihar Gombe kuma al’umma suka juya masa baya, to su sani, ba su cuci kowa ba sai kansu.
Allah ya kare mu da halayen ƙyashi da hassada, Amin.
_______________
Jama’a, yaya kuke ganin wannan al’amari? Shin ko Sheikh Pantami ya cancanci ya tsaya takarar Gwamna a Jihar Gombe? Ku bayyana ra’ayinku a Comment Section:













