Maraba Da Sabon Gidan Rediyon Afirka
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

•••••••
Shirye-shirye sun yi nisa, inda Sabon Gidan Rediyo Africa Radio International (ARI) zai fara gabatar da shirye-shiryensa a jibi Juma’a, 10 ga Oktoba, 2025.
Kamar yadda sanarwa ta gabata daga hukumomin gidan rediyon, kafa shi a wannan zamani, wani yunƙuri ne na gabatar da sabon salo a harkar watsa labarai a nahiyar Afirka. “Tasha ce, wadda burinta shi ne ta zama muryar Afirka ta gaskiya, wacce za ta kalato labarai daga sassa daban-daban na nahiyar Afirka, domin tattaunawa, ilmantarwa da wanzar da zaman lafiya.”
Sanarwar ta ƙara da cewa, ARI zai rika watsa shirye-shirye ta akwatin rediyo da kuma intanet, domin isa ga masu sauraro a duk faɗin duniya.
A cewar jagororin tashar, Africa Radio International za ta mai da hankali kan shirye-shiryen da suka shafi ci gaban siyasa, tattalin arziƙi, al’adu, da zamantakewar al’umma. Haka kuma za a riƙa gudanar da shirye-shiryen da ke inganta haɗin kai tsakanin ƙasashen Afirka, kamar kuma yadda za a riƙa tattauna al’amuran na hangen nesa dangane da Afirka. Tashar ta ce za ta kasance cibiyar haɗin kai tsakanin ‘yan jarida, masana, da masu ruwa da tsaki a fagen ci gaban Afirka.
Tashar ARI, namijin yunƙuri ne daga wasu zaƙaƙuran ‘yan jarida na Afirka, waɗanda a baya suka taba yin aiki a Gidan Rediyon Muryar Amurka (Voice of America), kafin Shugaban Ƙasa Donald Trump ya rufe shi a watannin baya.
An bayyana cewa hedikwatar ARI za ta kasance a Abuja, tare da rassa a wasu manyan biranen ƙasashen Afirka kamar Accra (Ghana), Nairobi (Kenya) da Johannesburg (Afrika ta Kudu).
_______________












