KWANKWASO BAI CIKIN WAƊANDA SUKA KAFA APC

•••••••
A wani saƙo da aka wallafa a shafin Buhari Reporters a Soshalmidiya, an bayyana cewa Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso ba ya daga cikin ‘yan siyasar da aka kafa Jam’iyyar APC da su. Ga abin da sakon yake cewa:
Ya mai girma Kwankwaso, gaskiyar magana ita ce, kai ba ka cikin waɗanda suka kafa jam’iyyar APC. An kafa jam’iyyar kuma aka yi mata rijista a hukumance a shekarar 2013, sannan kawai zuwa ƙarshen shekarar 2014 ka shiga tare da Amaechi, Wamakko, Nyako da Saraki. Amma Mu’azu Babangida Aliyu da Sule Lamiɗo sun ƙi shiga, suka zaɓi ci gaba da zama a Jam’iyyar PDP.
Ga halastattun jigajigan ‘yan siyasar da suka kafa Jam’iyyar APC:
√ Muhammadu Buhari, GCFR – daga ɓangaren CPC
√ Bola Ahmed Tinubu, GCFR – daga ɓangaren ACN
√ Rochas Okorocha – daga wani reshe na APGA
√ Kashim Shettima, Bukar Abba Ibrahim, Ibrahim Shekarau, da Yariman Bakura – daga ɓangaren ANPP
Ya Kwankwaso, ba ka taɓa zama cikin jagororin da suka kafa APC ba. Ka shiga ne bayan dangantakarka da Jonathan ta lalace har ya kai ga ba za ka iya zama a PDP ba, kuma kana buƙatar wata mafita ta siyasa.
Duk da haka, babu wanda zai iya musanta muhimmancin shigowarka cikin APC. Ka bayar da gagarumar gudummawa wajen nasarar jam’iyyar, har ta kafa gwamnati. Amma idan aka zo ga batun kafa ta – ba ka cikin masu kafawa.
Sai dai kuma, an yi maka sakayya bisa ƙoƙarinka, domin ka zama Sanata, Mataimakinka da kuka daɗe cikin aminci, Gabduje ya lashe kujerar Gwamna a Jam’iyyar APC, sannan kashi 99% na ’yan Majalisar Tarayya da ta Dokoki, daga jiharka dukkaninsu amintattunka ne.
________________













