Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris
Daga Wakilinmu
~~~~~~~
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ‘yan jarida ba a Nijeriya suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, kuma sun cancanci samun ingantacciyar rayuwa, yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu cikin sauƙi da walwala.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), a Abuja.
Idris ya ce wasu ‘yan jaridar ma sun rasa rayukansu wurin aikinsu. A kan haka ya ce zai yi iyakar ƙoƙarinsa domin inganta rayuwar ‘yan jarida a gwamnatance.
“Za mu yi ƙoƙarin ganin ana bai wa ‘yan jarida dukkan haƙƙoƙin da suka cancanta a ba su.
“Saboda suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, wani lokaci ma har rasa rayukansu suke yi, kamar yadda jami’an tsaro ke rasa nasu rayukan wajen tabbatar da tsaro.
“Sau da yawa za ku ga ‘yan jarida kafaɗa-da-kafaɗa a cikin jama’an tsaro idan sun fita yaƙi da ta’addanci. Da dama a cikinsu kan koma gida da raunuka a jikinsu.
“Kuma kun dai ga yadda ɗan jarida ya rasa ransa a Zamfara saboda hare-haren ‘yan bindiga.
“To duk irin waɗannan ba abubuwan jin daɗi ba ne a ce a matsayina na Ministan Yaɗa Labarai wannan na faruwa. Ina so na ga ƙarshen wannan matsalar,” in ji Idris.
Sannan kuma ya kawo hanzarin dalilin da ya sa gwamnati ba za ta tsame ‘yan jarida ta yi masu ƙarin albashi su kaɗai ba. Ya ce akwai muhimmancin a duba ainihin yadda aikin nasu ke da tasiri da haɗari, domin a magance matsalolin da suke fuskanta.
“Ni a sahun gaba nake na masu hanƙoron ganin rayuwar ‘yan jarida ta inganta. Kuma ina taka-tsantsan da sanin cewa suna aiki ne cikin da’irar iyakar gejin tattalin arziki ƙasarmu.
“Don haka ya zama tilas mu dubi wannan lamari baki ɗaya, domin a ƙarshe a yi mana kyakkyawar shaidar ‘yan ƙasa nagari.”
~~~~~~~













