• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, July 26, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris

Daga Wakilinmu by Daga Wakilinmu
October 18, 2023
in Labarai
0
Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris

Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai

32
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris

Daga Wakilinmu

Related posts

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta

July 7, 2026
Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026

~~~~~~~

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ‘yan jarida ba a Nijeriya suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, kuma sun cancanci samun ingantacciyar rayuwa, yadda za su samu damar gudanar da ayyukansu cikin sauƙi da walwala.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), a Abuja.

Idris ya ce wasu ‘yan jaridar ma sun rasa rayukansu wurin aikinsu. A kan haka ya ce zai yi iyakar ƙoƙarinsa domin inganta rayuwar ‘yan jarida a gwamnatance.

“Za mu yi ƙoƙarin ganin ana bai wa ‘yan jarida dukkan haƙƙoƙin da suka cancanta a ba su.

“Saboda suna aiki a cikin mawuyacin yanayi, wani lokaci ma har rasa rayukansu suke yi, kamar yadda jami’an tsaro ke rasa nasu rayukan wajen tabbatar da tsaro.

“Sau da yawa za ku ga ‘yan jarida kafaɗa-da-kafaɗa a cikin jama’an tsaro idan sun fita yaƙi da ta’addanci. Da dama a cikinsu kan koma gida da raunuka a jikinsu.

“Kuma kun dai ga yadda ɗan jarida ya rasa ransa a Zamfara saboda hare-haren ‘yan bindiga.

“To duk irin waɗannan ba abubuwan jin daɗi ba ne a ce a matsayina na Ministan Yaɗa Labarai wannan na faruwa. Ina so na ga ƙarshen wannan matsalar,” in ji Idris.

Sannan kuma ya kawo hanzarin dalilin da ya sa gwamnati ba za ta tsame ‘yan jarida ta yi masu ƙarin albashi su kaɗai ba. Ya ce akwai muhimmancin a duba ainihin yadda aikin nasu ke da tasiri da haɗari, domin a magance matsalolin da suke fuskanta.

“Ni a sahun gaba nake na masu hanƙoron ganin rayuwar ‘yan jarida ta inganta. Kuma ina taka-tsantsan da sanin cewa suna aiki ne cikin da’irar iyakar gejin tattalin arziki ƙasarmu.

“Don haka ya zama tilas mu dubi wannan lamari baki ɗaya, domin a ƙarshe a yi mana kyakkyawar shaidar ‘yan ƙasa nagari.”
~~~~~~~

Previous Post

Betaran Biu Janar Buratai Ya Samu Sarautar ‘Baakoren Akure’

Next Post

Za Mu Sake Dasa Wa Al’ummar Nijeriya Ɗabi’ar Yarda Da Kalaman Shugabanni – Minista Idris

Related Posts

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta
Labarai

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Karrama Tsofaffin Dakarunta

July 7, 2026
Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Next Post
Za Mu Inganta Rayuwa Da Ayyukan ‘Yan Jarida – Minista Idris

Za Mu Sake Dasa Wa Al'ummar Nijeriya Ɗabi'ar Yarda Da Kalaman Shugabanni - Minista Idris

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

Book Launch Seeks to Rewrite Lassa’s Story, Preserve Cultural Heritage

July 9, 2026

June 27, 2025
Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

Littafin Rayuwar Fitacciyar ‘Yar Jarida Jamila Tangaza

April 11, 2026
ABDU SALA MALUMFASHI: MUN YI RASHIN ƊAN UWA/ABOKI

ABDU SALA MALUMFASHI: MUN YI RASHIN ƊAN UWA/ABOKI

June 20, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • General Buratai to Marry Off His Daughter Today
  • Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya
  • Saƙon Godiya Da Bangajiya

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

July 25, 2026
Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

July 24, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.