Matsalolin Arewa: Lallai Ne Mu Yi Karatun-Ta-Natsu
Daga Zainab Ahmad Mohammed

•••••••
Arewa na buƙatar gyaran zuciya da gaske kuma kowa ya fara da gyara kansa da gidansa.
Babu inda aka halalta maka aure-aure idan ka san ɗaya ma ba za ka iya kula da ita ba. Babu inda aka aminta maka ka haifi yaran da ka san ba za ka iya ɗaukar nauyinsu ba. Idan har ka iya yin aure, to ya zama dole ka iya sauke duk haƙƙin aure da Allah ya ɗora maka kuma dole ka ɗauki nauyin duk ɗan da ka yi silar zuwansa duniya.
Yaran da ake haihuwa ba su da laifi, ku iyayen ne ke da laifi kuma kuka gaza saboda son zuciya da rashin sanin ciwon kai. Kuma sai Allah ya tambaye ku a kan gazawar ku.
Sannan ka sani, muddin dai kana cikin masu irin wannan mummunar ɗabi’a, to kana cikin waɗanda suka jawo wa Arewa matsala. Haka kuma ka ba da gagarumar gudunmowa a duk matsalolin da ke addabar Arewa.
Lokaci ya yi da za mu tashi tsaye mu gyara tsarin aure, ilimi da tarbiyya saboda nan ne tushen komai.
Ina ba da haƙuri idan maganganuna sun ɓata wa wani k wata rai. Ita gaskiya dama ɗaci ke gare ta.
_______________












