TARON JIGAJIGAN KATSINA ALHERI NE
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, a ranar Lahadi da ta gabata, (14 ga Satumba, 2025) ya jagoranci babban taron shawarwari da ya haɗa manyan mutane na jihar domin tattaunawa kan harkokin tsaro, mulki da cigaba.
Taron ya samu halartar dattawa, sarakuna, shugabannin addini, tsofaffin hafsoshin tsaro, da fitattun ’ya’yan Katsina daga gida da waje – dukkaninsu sun haɗu wajen duba nasarori, nazarin ƙalubale, tare da tsara dabarun tabbatar da zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.
A jawabinsa na bufewa, Mataimakin Gwamna Faruk Lawal Joɓe ya bayyana cewa a ƙarƙashin manufar Gwamnatin Radda ta “Gina Makomarka,” gwamnatin jihar ta samar da ayyukan yi kimanin guda 35,903, a fannoni daban-daban, ciki har da ɗaukar malaman makaranta, naɗin dagatai, da kuma ɗaukar dakarun tsaro na al’umma, ’yan banga, mafarauta da shugabannin addini da suke taka muhimmiyar rawa wajen samar da zaman lafiya.
A sahun gaba na jigajigan da suka kasance a taron, sun haɗa da tsohon Gwamna Rt. Hon. Aminu Bello Masari; dattijo kuma jigo na siyasa Sanata Abu Ibrahim; hamshaƙin ɗan kasuwa Alhaji Ɗahiru Barau Mangal; Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk; Sanata Ibrahim Ida, Wazirin Katsina; da kuma Sanata Hadi Sirika.
Haka kuma akwai Ministan Gidaje da Cigaban Birane, Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Mai Ba wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan Tsare-tsare, Hajiya Hadiza Bala Usman.
Sauran muhimman mutanen da suka halarci taron sun haɗa da Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan DSS; Alhaji Aminu Maida, EVC na NCC; Jakada Ahmed Rufai, Sardaunan Katsina kuma tsohon Daraktan NIA; dattijo Sanata Abubakar Mamman Ɗanmusa; Injiniya Abubakar Yar’adua, tsohon Manajan Darakta na NNPC; Mai Shari’a Sadiq Abdullahi Mahuta, Galadiman Katsina kuma Hakimin Malumfashi; Rt. Hon. Nasir Yahya Daura, Kakakin Majalisar Dokoki ta Jihar Katsina; Sanata Abdulaziz Yar’adua; Sanata Muntari Dandutse; da Sanata Nasiru Zangon Daura. Ɓangaren shari’a ya samu wakilci daga Mai Shari’a Musa Danladi, Babban Jojin Jihar Katsina.
Ɓangaren sojoji kuwa ya samu halartar manyan jami’an da suka yi ritaya: Kanal Abdulmumini Aminu, Brig. Janar Ahmed Daku, Kanal U.F. Ahmed, Brig. Janar Maharazu Tsiga (tsohon DG na NYSC), Air Commodore Yusuf Anas, AVM Sadiq Kaita, Major Janar Junaid Bindawa, da Brig. Janar Usman Sani Kukasheka, tsohon Jami’in Watsa Labarai na Sojojin Najeriya, da sauransu.
Sauran manyan baƙi sun haɗa da SGS Barr. Abdullahi Garba Faskari; Hon. Abdulƙadir Mamman Nasir, Shugaban Ma’aikata; Abdullahi Aliyu Turaji, Babban Sakataren Fada na Gwamna; tsoffin Mataimakan Gwamna — Alhaji Tukur Jikamshi, Q.S. Mannir Yakubu, da Alhaji Sirajo Damari; Barr. Ahmed El-Marzuk; Injiniya Nura Khalil; Alhaji Kabir Mashi, tsohon Shugaban FIRS; Alhaji Tukur Bello Ingawa, tsohon Shugaban FCSC; Farfesa Saddique Mohammed na Jami’ar ABU Zaria; Farfesa Sadiq Isah Radda na BUK; Farfesa Mansur Malumfashi na ATBU; Farfesa Suleiman Ahmed Isah na UDUS; Dr. Bashir Ruwan Godiya daga Gamayyar Ƙungiyoyin Kare ‘Yancin Ɗan Adam (CSOs) tare da shugabannin manyan makarantu a jihar.
Haka kuma akwai Injiniya Bala Banye, Kwamishina a Gwamnatin Tarayya, a NPC; Hon. Jabiru Salisu Abdullahi Tsauri, Shugaban Kasa/CEO na NEPAD; Hajiya Mariya Abdullahi; Hajiya Indo Mohammed; Farfesa Badamasi Lawal Charanchi, Shugaban NSIPA; Magatakarda Kabir Yahaya; da Injiniya Bello Lawal Yanɗaki, Shugaban Ƙungiyar ALGON na ƙasa.
Dukkan ‘yan Majalisar Wakilai na Jihar Katsina a Majalisar Tarayya, manyan jami’ai na Majalisar Dokokin Jihar Katsina, wasu daga cikin mambobin Majalisar Zartarwa, shugabannin addinai, wakilan klƙungiyar kwadago da na kasuwanci, da ƙungiyoyin fararen hula da na al’umma, tare da ‘yan kasuwa, duk sun halarta wajen taron.
Babu shakka, muddin dai gwamnati ta yi amfani da muhimmin shawarwarin da aka gabatar a yayin wannan taro, to kuwa zai zama alheri ga al’ummar Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.
__________













