Ruhin Bukar Usman
(Wake)
Khalid Imam
*****

Ganga ta jikin Bukar ce,
Ke zaune garin Abuja,
Ruhin Bukar Usman duka
Ni na shaida da kaina,
Suna Biu cibiyarsa,
Ni Khalidu ni da kaina,
Zahiran na gani idona.
Garin Biu ne mahaifa,
Gun Bukar Usmanu gwarzo,
Ita dawa tushiyarta,
Asalinta da salsalarta,
Jijiyar bishiya gidanta,
Ko tai inuwa da rassa,
A maƙota babu shakka.
Na je Biu na ziyarci,
Gidan su Bukar gwanina,
Ɗan dangi ne cikakke,
Shi ba inuwa ba ne ba,
Ta giginya ko alama,
Ya amfana wa dangi,
Kogi ne shi ga kowa.
A garin Biu babu shakka,
Bukar Usmanu giwa,
Rijiya na tsakiyar gari ne,
Kowa na shan ruwanta,
Mutan Biu ni Imamu,
Sun shaida min da kansu,
Bukar ɗa ne na kishi.
Dattijawa har saraki,
Malaman Biu har matasa,
Mata da maza da yara,
Sun yaba wa Bukar da gaske,
Jinjina sun yi wa ɗansu,
Darajar Biu ya ɗaga ta,
Duniya duka ta yi shaida.
Ƙasar Biu tarihinta,
Bukar Usman fasihi,
Ya taskace duk a kundi,
Shi yai aikin da kansa,
Duniya yau ta karanta,
Bukar ɗa ne na karimi,
Ɗa mai kishin mahaifa,
Jarin sana’a ga mata,
Maza manya matasa,
Bukar Usmanu Dokta,
Ya ba dubbai da kansa,
A Garin Biu ya yi bohol,
Ruwa ya ba maƙota,
Bukar bai manta tushe.
Irin noma da taki,
Na zamani a kyauta,
Bukar ya raba na noma
Domin bunƙasa noma,
Amfani yai yabanya,
Arziki jama’a su samu,
A ƙasar Biu kewayenta.
Ilimin tata da gyara,
Na mai na gyaɗa da sannu,
Kamfaninsa Bukar ya kawo,
Ƙasar Biu don manoma,
Kishin jama’a ƙasarsa,
Tasa shi hakan da kansa
Bukar gwarzo na nuni.
__________
(HM) Khalid Imam
Garin Biu
5.50 NY
11 ga Afirelu, 2024












