Jaafar Jaafar Da ‘Yan Siyasar Kano: Ashe Wanzami Ba Ya Son Jarfa?
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

_______________
Ga duk mai bibiyar al’amuran siyasa, musamman a Jihar Kano, zai cika da mamaki yadda wasu ‘yan siyasa ke nuna son rai da ƙeƙashewar zuciyar ɗaure wa ƙarya gindi. Babban abin da ke faruwa a yanzu, tsakanin ɗan jarida kuma mawallafin jaridar Daily Nigerian, Malam Ja’afar Ja’afar da Gwamnatin Jihar Kano, ya isa misali.
A lokacin da shi Ja’afar ya kafa suna da tarihin bankaɗo almundahana da zurmuƙen da ‘yan siyasa da masu mulki, musamman a Jihar Kano suke aikatawa, su kuma sai suka zama ‘yan a bi Yarima a sha kiɗa.
Yadda abin yake shi ne, idan yau ya bankaɗo wani al’amari mara daɗi a kan ‘yan Gandujiyya, sai ‘yan Kwankwasiyya su yi ta kaɗa masa tambura, suna kwarzanta shi, tare da yaba masa cikin murna da jin daɗi. Haka kuma, idan reshe ya juye da mujiya, ya bankaɗo wani jami’in Gwamnatin Kwankwasiyya, sai kuma ‘yan Gandujiyya su kama murna, a yayin da su kuma za su yi ta kai gwauro da mari suna la’antarsa, tare da barazanar kai shi kotu. Akwai misalai masu yawa a kan haka.
A can baya, jaridar Ja’afar ta taɓa buga rahoton yadda aka zargi Sarki Kano, Muhammadu Sanusi II da lalata dukiyar Masarautar Kano, kimanin Naira biliyan 3.4, tsakanin shekarar 2014 zuwa 2017. ‘Yan siyasa ɓangaren Gandujiyya sun yi murna da wannan. A yayin da su kuma ‘yan Kwankwasiyya suka gune.
A na nan kuma sai ga wata sabuwar wainar daga tandar Ja’afar, wadda ya toya a shekarar 2018. A wannan karon, wani faifan bidiyo ne ya wallafa, inda aka nuno Gwamnan Jihar Kano na lokacin, Alhaji Abdullahi Umar Ganduje yana amsar daloli da aka ƙiyasta sun kai Dala miliyan biyar. An yi zargin cewa rashawa ce yake amsa daga hannun wani ɗan kwangila.
Ai kuwa abin nema ya samu, matar ɗan Kwankwasiyya ta haifi jar hula. A sakamakon wannan bankaɗa ta bidiyo, babu sunan da ba su raɗa wa Ganduje ba kuma babu yabon da ba su yi wa Ja’afar ba. Su kuwa ‘yan Gandujiyya, har matakin Shari’a sai da suka ɗauka. Daga bisani ma, wannan al’amari sai da ya tilasta masa yin gudun hijira zuwa Ingila.
Tafiya sannu-sannu kwana nesa. Haka ne har Allah ya kawo mu watan Agusta da ya gabata, inda ɗan jarida Ja’afar ya sake bamkaɗo wata ƙumbiya-ƙumbiyar, wacce ta shafi Gwamnatin Jihar Kano, a ƙarƙashin Gwamnan Kwankwasiyya, Abba Kabir Yusuf. A wannan karon, jaridar ta wallafa zargin Darakta Janar Protocol na Gidan Gwamnatin Jihar Kano, Abdullahi Rogo da karkatar da Naira biliyan 6.5.
Kamar yadda tafiyar ta saba, yau ma ba ta canza zane ba, domin kuwa a halin da ake ciki Gwamnatin Jihar Kano da ‘yan Kwankwasiyya sun far wa Ja’afar ta hanyoyi da dama. Wasu suna zagi, wasu suna la’anta, a yayin da ita kuma gwamnati ta kai koke ga ‘yan sanda, cewa a bincike shi da laifin ɓata suna, kamar kuma yadda take shirin kai shi ƙara kotu!
A taƙaice dai, wanzami ba ya son jarfa. Ja’afar yana aikinsa na jarida, su kuma ‘yan siyasar Kano, kowane ɓangare bai so a ce an bankaɗo ɓarnar da yake aikatawa.
__________
Jama’ar Allah, yaya kuke ganin wannan al’amari? Ku bayyana ra’ayinku a Comment Section:












