• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Saturday, May 2, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Labarai

₦8000 Ba Za Ta Sayi Tiyar Masara 10 Ba – Sarkin Samarin Galadima

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
July 16, 2023
in Labarai
0
₦8000 Ba Za Ta Sayi Tiyar Masara 10 Ba – Sarkin Samarin Galadima

Abdul'aziz Sarkin Samarin Galadiman Katsina

16
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

₦8000 Ba Za Ta Sayi Tiyar Masara 10 Ba – Sarkin Samarin Galadima

Mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Sarkin Samarin Galadiman Katsina, Abdul’aziz ibni Abdul’aziz ya bayyana cewa akwai abin dubawa da tsarin tallafin da Gwamnatin Tarayya ke shirin aiwatarwa, na bayar da Naira dubu takwas ga alakawan Nigeria miliyan 120 da nufin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur da ta yi a watan Mayu da ya gabata.

Related posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026

Tun farko, Taskar Gizago ta tambaye shi abin da zai ce game da cire tallafin fetur da gwamnatin ta yi.

Abdul’aziz ya ce “Cire tallafin mai abu ne mai kyau sai dai gwamnatinmu ta APC ba ta yi shi daidai da lokacin da ya kamata ba. Dalilina kuwa shi ne, ya kamata a ce an fara yin shirin kwantar wa talakawa da hankali kamin cire tallafi, ba wai sai yanzu ba da ‘yan kasuwarmu ke jiran irin wannan damar, domin su muzguna wa talakawa.”

Ya ce dan ka dubi Arewaci, musamman Arewa Maso Gabas da Arewa Maso Yamma, da yawan mutane suna kokawa a kan tsadar rayuwa da cire tallafin mai ya haifar masu a wannan lokacin da rayuwar da ƙyar ake yin ta.

Game da tallafin ₦8000 kuwa, mai sharhin cewa ya yi “Maganar shirin rage talauci da suke faɗi ₦8000, wadda ba ta sayen tiyar masara goma, kuma ta hannu su wa kuɗin za su fito, domin a bayar su isa inda ake so su je?”

Ya ƙara da cewa, “Idan ka kalli shugabaninmu, musamman waɗannan da suka shude da waɗanda suke a kan karagar mulki, wace rawa suka taka ko suke takawa don ganin an samu zuba jari a jihohin Arewacin Nigeria?”

Game da matsalar Arewa, ya ce har kullum yana ganin ita ce ta rashin kamfanoni ko kuma ba a maida hankali ga ‘yan kasuwar waje, su zo Arewacin Nigeria don sarrafa kayansu.

“Idan ka kalli 6arewa a kan maganar waken suya kaɗai da riɗi, daga nan ake ɗauka a kai Lagos a sarrafa su kuma a dawo da mansu mu saya,” inji shi.

Taskar Gizago ta tambaye shi cewa, shi a shawararsa, tun da raba ₦8000 ga talakawa ba zai yi tasiri ba, wane mataki ya kamata a ɗauka na rage kaifin talauci a Nigeria?

“Rashin tasiri ko alfanun wannan abu sh ine, idan ka duba inda matsalar take, ba nan ake maida hankali ba.
Yanzu a Jihar Katsina ko Kano kaɗai, talakawan da suke nan wajen, sun fi talakawan da ke Kudu gaba ɗaya yawa. Amma kuma za ka ga cewa taimakon ya tafi Kudu fiye da Arewacin Nigeria.

“Ni yanzu inda zan bai wa Gwamna Dikko Radda shawara, wallahi sai in ce ya amshe duk wani fili da aka bayar don gina wani kamfani amma abin baiyi tasiri ba. Saboda da yawansu sun amshi filayen nan kyauta a hannun gwamnatin da ta gabata da sunan za su yi kamfanoni kuma sun kewaye da katanga sun manta da su kawai.”

Previous Post

Dogo Na Magayaƙin Kano Ya Angwance

Next Post

A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

Related Posts

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi
Labarai

Gobe Gwamna Dikko Raɗɗa Zai Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Al’umma Da Muntari Sagir Ya Gina A Malumfashi

April 19, 2026
Ɓatanci Ga Manzon Allah: Musulmi Sun Buƙaci Gwamnati Ta Hukunta Fasto Emmanuel Garba?
Labarai

Fasto Ɗan Ƙungiyar Hausawan Bogi Da Ya Zagi Annabi Ya Ɓoye

April 15, 2026
Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina
Labarai

Sheikh Mutawakkil Mustapha Ya Zama Alƙalin Kotun Shari’a ta Ɗaukaka Ƙara ta Jihar Katsina

February 13, 2026
Next Post
A Mako Ɗaya Kacal: Jami’an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

A Mako Ɗaya Kacal: Jami'an NDLEA Sun Yi Wawan Kamun Muggan Ƙwayoyi A Abuja, Lagos Da Sassan Nigeria

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Burina In Shiga Aljanna A Sanadiyyar Waƙa – Alkantamawy

Burina In Shiga Aljanna A Sanadiyyar Waƙa – Alkantamawy

June 21, 2023
Yau Aka Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Al’ummar Jihar Katsina

Yau Aka Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Al’ummar Jihar Katsina

October 10, 2023
GURƁATACCEN HATSI: An Ja Hankalin Hukumomin Jihar Katsina

GURƁATACCEN HATSI: An Ja Hankalin Hukumomin Jihar Katsina

August 20, 2023
Jinjina Da Yabo Ga Nagartaccen Shugaba: Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

Jinjina Da Yabo Ga Nagartaccen Shugaba: Malam Labiru Musa Ƙafur, mni

October 29, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana
  • Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)
  • General Buratai (A Poem)

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

Dokta Bukar Usman Ya Wallafa Sabbin Littattafai 6 A Bana

April 28, 2026
Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

Exposing Plans of Fake Hausa Activists & Ba-Zata Mischief Mongers to Cause Confusion and Discord in Northern Nigeria (11)

April 27, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.