Sunanta Ummu-Khulsum
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Yau Lahadi, 01-04-1448 (Hijiriyya), 13-09-2026 (Miladiyya), kwana bakwai daidai da ƙaruwar haihuwa da na samu. Alhamdu Lillah! A yau na raɗa mata suna UMMU-KHULSUM!
Ummu-Khulsum (أم كلثوم) suna ne daga cikin sunayen da aka sani sosai a tarihin Musulunci. Ɗaya daga cikin ’ya’yan Manzon Allah ﷺ ita ce Ummu-Khulsum bint Muhammad ﷺ.
Sunan ya ƙunshi kalmomi biyu: Ummu (أمّ), ma’anarsa, uwa. Sai kuma Khulsum (كلثوم), wanda suna ne na Larabci na gargajiya kuma ana danganta shi da kyakkyawar fuska, cikar kumatu ko nama a fuska, musamman wajen bayyana kyawun mace.
Saboda haka, Ummu-Khulsum a matsayin suna na mace yana ɗauke da ma’ana mai kyau da daraja kuma ana iya fahimtarsa a matsayin “Mace Mai Kyakkyawar Fuska/Cikakkun Kumatu.” Suna ne na girmamawa na Larabawa.
Ummu-Khulsum bint Muhammad ﷺ ita ce ’yar Manzon Allah ﷺ da Sayyida Khadijah (RA). Ta kasance ƙanwar Zainab, Ruƙayyah da Fatimah (RA), kuma ta auri Sayyidina Uthman bn Affan (RA) bayan rasuwar ’yar uwarta Ruƙayyah (RA).
A ɓangare na biyu, Ummu-Khulsum suna ne na yayata (Gude), wacce ta rasu shekaru biyu da suka gabata. Don haka, wanan suna na ɗaya daga cikin hanyar tunawa da ita. Allah ya ji ƙan ta da rahama.
__________













