BATUN SASANCI DA ‘YAN BINDIGA A JIHAR KATSINA
Daga Bashir Yahuza Malumfashi

__________
Allah da ikonsa, mun shiga sabon yanayi, inda Gwamnatin Jihar Katsina ta amince kuma take ƙulla sasanci da ‘yan bindigan da suka daɗe suna zaluntar al’umma.
Tun daga fara wannan ibtila’i na ‘yan bindiga, babu wani da zai iya lissafta iya ƙimar asarar da al’umma suka yi. Lissafi ba zai yiwu ba, idan aka yi la’akari da yawan rayukan da suka salwanta, da yawan matan da aka tozarta da yawan yaran da aka mayar marayu, balle kuma yawan dukiyar da aka lalata.
Wani abu da yake sosa mani rai game da wannan sasancin shi ne, babu tabbacin zai ɗore ko kuma ya haifar da ɗa mai ido. Kamar yadda batun yake, ba a cutar mumini sau biyu kuma ya amince da na uku. Zan iya tunawa, a can baya, zamanin mulkin Gwamna Aminu Bello Masari, an yi sulhu da ‘yan bindiga, su Buharin Daji da kininsa, amma sasancin bai yi ƙarko ba, sai da lamarin ya dawo ɗanye kuma ya ci gaba da gudana har zuwa yau da ake batun wani sulhun.
Wani abin tambaya kuma shi ne, shin wannan sulhu, me ya sa su ‘yan bindiga kaɗai yake amfana? Su ne fa suke illata al’umma kuma su ake tarairaya. To su al’ummar da aka kassara, aka mayar da su marayu, zawarawa, aka mayar da su kwana a sansanonin ‘yan gudun hijira, shin me aka yi masu ko ake shirin yi masu domin sauƙaƙa masu rayuwa?
Kodayake Allah shi ne mai yadda ya so, zai iya kawo mana canji daga kowane lungu. Muna roƙonsa da sunayensa tsarkaka – Allah ya sa wannan sulhu ya zama alheri, ya ɗiga aya ga wannan mummunan yanayi da muka samu kanmu a ciki. Amin-Summa-Amin.
_______________
Al’ummar Allah, me za ku ce game da wannan lamari na sulhu? Kuna da wata shawara ko kira ga gwamnati dangane da lamarin? Ku bayyana a Comment Section:













