• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Sunday, September 20, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Gizago

Ayyukan Alheri Daga Gidan Amana

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
September 5, 2026
in Gizago
0
Ayyukan Alheri Daga Gidan Amana

Dakta Haruna Maiwada da wasu ayyukansa na alheri

15
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Ayyukan Alheri Daga Gidan Amana

Daga Bashir Yahuza Malumfashi

Related posts

SUNANTA UMMU-KHULSUM

SUNANTA UMMU-KHULSUM

September 13, 2026
HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

September 12, 2026
Dakta Haruna Maiwada da wasu ayyukansa na alheri


__________
Taimakon al’umma, musamman raunana, mabuƙata, marasa galihu da faƙirai, yana daga cikin manyan ayyukan alheri da Musulunci ya ƙarfafa. Al’umma ba ta ƙarfi da dukiyar masu hannu da shuni kaɗai, sai dai idan waɗanda Allah ya hore wa dukiya suka kasance masu tausayi da tallafa wa waɗanda suke cikin buƙata.

Allah Maɗaukakin Sarki a cikin Alƙur’aninsa mai girma, Suratul Ma’idah (5:2) ya ce: “Ku yi wa juna taimako a kan alheri da taƙawa, kada ku yi wa juna taimako a kan zunubi da zalunci.” Wannan aya tana nuna cewa taimakon juna a kan abin da yake na alheri da amfani ga mutane wata hanya ce ta samun yardar Allah.

Bisa ga wannan gwadabe, ya zama wajibi a ambata sunan Jagoran Gidan Amana a Jihar Katsina, Alhaji Haruna Maiwada, Sadaukin Kaita kuma Ɗan Amanar Katsina da babbar murya; musamman yadda a kodayaushe yake saka farin ciki a zukatan mabuƙata da raunana, har ma da sauran al’umma.

A ranar Lahadin da ta gabata, 30 ga watan Agusta 2026, a irin wannan aiki da ya saba na jin ƙari, ya ƙaddamar da wasu muhimman ayyukan jin ƙan guda biyu. Ayyukan sun haɗa da raba kekunan guragu guda 100, a Ƙananan Hukumomin Katsina da Kaita, domin sauƙaƙa masu sufuri da samar masu walwala da jin daɗi. Haka kuma, ya bai wa kowannensu Naira dubu goma.

Haka kuma, duk dai a Lahadin da ta gabata, Ɗan Amana ya ƙaddamar da rarraba baburan hawa (Roba-Roba) guda 50 ga matasa, waɗanda suke tare da shi wajen hidimar siyasa da ta rayuwar yau kullum.

Wani al’amari na jin ƙai daga Dakta Maiwada ya sake faruwa a wanshekaren da ya yi wannan abin alheri, inda ya samu labarin wani matashi da aka sace wa abin hawa. Nan take ya ba shi kyautar sabon babur shi ma.

Irin wannan aiki sai mai ƙarfin imani, wanda yake bin umurnin Allah. A Alƙur’ani mai girma, Suratu Ali ‘Imrana (3:92), Allah ya yi magana kai tsaye game da kulawa da mabuƙata da raunana, inda ya ce: “Ba za ku sami kyautatawa ba har sai kun ciyar daga abin da kuke so; kuma duk abin da kuka ciyar, to lalle Allah Masani ne gare shi.”

Wannan aya tana koyar da mu cewa ainihin kyautatawa ba wai mutum ya bayar da abin da ba ya buƙata kawai ba ne; a’a, ya bayar daga abin da yake so kuma yake daraja. Don haka, ya kamata masu hali su yi koyi da Dakta Maiwada, su sani cewa dukiyar da suke da ita, amana ce daga Allah, kuma akwai haƙƙoƙin wasu mutane a cikinta.

A wani Hadisi da aka ruwaito daga Jabir (ra), Manzon Allah (saw) yana cewa: “Mafi alherin mutane, shi ne wanda ya fi amfani ga mutane.”

Ma’ana dai ita ce, darajar mutum ba ta ta’allaƙa ne kawai da yawan dukiyarsa, muƙaminsa ko shahararsa ba, sai dai da irin amfanin da yake yi wa sauran mutane. Wanda yake amfani da dukiyarsa wajen ciyarwa, taimakon marar lafiya, ɗaukar nauyin karatu ga marasa hali, tallafa wa maraya ko taimakon wani da ke cikin tsananin rayuwa, yana barin kyakkyawan tasiri a cikin al’umma.

Haka kuma a Sahih Muslim, Hadisi mai lamba 2699, Manzon Allah (saw) ya kwaɗaitar da masu hali da su taimaki mabuƙata, yana bayyana girman ladan wannan aiki. Ya ce: “Duk wanda ya yaye wa mumini wata damuwa daga cikin damuwoyin duniya, Allah zai yaye masa wata damuwa daga cikin damuwoyin ranar alƙiyama kuma wanda ya sauƙaƙa wa wanda yake cikin tsanani, Allah zai sauƙaƙa masa a duniya da Lahira.”

Wannan babban kira ne ga masu arziki da su yi amfani da abin da Allah ya ba su wajen rage wahala da ƙuncin da mutane suke ciki. Dukiya ba ta zama abin alfahari kawai ba, tana iya zama hanyar samun rahamar Allah idan aka yi amfani da ita wajen taimakon bayinsa.

Bisa ga wannan hujja, muna roƙon Allah ya ƙarfafa himmar Dakta Maiwada, ya biya masa buƙatunsa na alheri, duniya da lahira. Allah ya sa sauran attajirai su yi koyi da ayyukan alherin da yake shuka wa al’umma a kullum.
__________

Previous Post

Zuwa Ga Sanata Ahmad Babba Kaita

Next Post

Matasa Ku Ƙara Himma Domin Dogaro Da Kai – Gwamna Radda

Related Posts

SUNANTA UMMU-KHULSUM
Gizago

SUNANTA UMMU-KHULSUM

September 13, 2026
HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1
Gizago

HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

September 12, 2026
Zuwa Ga Sanata Ahmad Babba Kaita
Gizago

Zuwa Ga Sanata Ahmad Babba Kaita

September 4, 2026
Next Post
Matasa Ku Ƙara Himma Domin Dogaro Da Kai – Gwamna Radda

Matasa Ku Ƙara Himma Domin Dogaro Da Kai - Gwamna Radda

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

YADDA SHARA TA MAMAYE BIRNIN KATSINA

YADDA SHARA TA MAMAYE BIRNIN KATSINA

September 18, 2023
BAKIN JAƁA (5)

BAKIN JAƁA (5)

September 24, 2025
Wawason Dukiyar Al’umma: Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Ba’asin Tsohon Gwamna Matawalle

Wawason Dukiyar Al’umma: Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Ba’asin Tsohon Gwamna Matawalle

June 3, 2023
Yau Maulidin Katsina First

Yau Maulidin Katsina First

July 10, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso
  • JAGORA: Leader of the Masses
  • MALAM SULE LAMIDO: Jagoran Talakawa Ya Cika Shekaru 78

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

Zan Iya Yafe Wa Gwamna Abba – In Ji Kwankwaso

September 20, 2026
JAGORA: Leader of the Masses

JAGORA: Leader of the Masses

September 17, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.