• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, January 16, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Adabi

YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
August 31, 2023
in Adabi
0
YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Littafin Yamtarawala

40
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG

Littafin wasan kwaikwayo mai taken “Yamtarawala – The Warrior King (Yamtarawala – Jarumin Mayaƙin Sarki) ya kama hanyar lashe Gasar Adabi ta bana, wadda Kamfanin Sarrafa Iskar Gas na Najeriya (NLNG Limited) ke shiryawa duk shekara.

Related posts

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 23, 2025
Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

December 6, 2025

Littafin, wanda marubuci kuma ɗan jarida Henry Akubuiro ya rubuta, ya samu nasarar tsallake shingen alƙalan gasar, inda ya kasance ɗaya daga cikin uku da za su fafata domin fitar da na ɗaya da na biyu da kuma na uku.

A ranar Talatar da ta gabata (29-08-2023) ce, Shugabar Kwamitin Gasar, Farfesa Akachi Adimorah ta sanar da sunayen littattafan guda uku. Sauran biyun sun haɗa da littattafan wasan kwaikwayo mai taken “For Grit” na marubuci Obari Gomba da kuma “The Ojuelegba Crossroads” wanda Abideen Abolaji Ojomu ya rubuta.

Kamar yadda kwamitin ya bayyana ingancin littattafan uku da suka yi nasara, ya ce tsarin wasannin kwaikwayon sun ciri tuta, musamman ta fuskar zubi da tsari, zaɓen kalmomin da suka dace da al’ada da kuma ingancin labari, wanda za a iya nunawa a aikace, a fim ko a daɓe. Ya ƙara da cewa littattafan sun cancanci ƙima ta musamman, a fagen adabi, waɗanda suka haɗa dukkan wata ƙwarewa a sarrafa alkalami da hikima, irin dai wadda kwamitin na Gasar Rubutun Adabi ta Najeriya ke buƙata.

Shugabar Kwamitin ta ce, alƙalan gasar sun yaba wa littafin “For Grit” da cewa babban wasan kwaikwayo ne da ya gamsar fiye da ƙima. Tsarin warware jigon labarin yana kama hankali, tsarin bugun littafin ya ƙayatar sosai.

Game da littafin “The Ojuelegba Crossroads” kuwa Farfesa Akachi ta ce alƙalan sun gamsu da shi sosai. Sun ce ya kawo bayanan da suka danganci zamantakewar al’umma da siyasa. Irin yadda marubucin ya tunkari bayyana faɗi-tashin al’umma na yau da kullum, da yadda suke ɗaukar matakan daidaita rikitattun al’amuran rayuwarsu domin dacewa, su ne suka inganta littafin, suka ba shi babbar daraja.

Da Shugabar Kwamitin ta zo bayani game da littafin “Yamtarawala – The Warrior King” na Henry Akubuiro kuwa, cewa ta yi: “Littafin ya ɗauki hankalin alƙalan gasar saboda tsarinsa mai hawa da sauka da nuna gwanintar wasan kwaikwayo. Yadda aka tsara shi bisa dacewa da inganci, zai sauƙaƙa ɗabbaƙa shi a aikace, a daɓe ko ma a allon fim. Irin yadda marubucin ya warware ƙunshiyar labarin, yana riƙe mai karatu cikin ƙayatarwa da saka nishaɗi.”

Baya ga kwamitin shirya gasar, marubutan uku da suka yi nasara sun samu yabo da jinjina daga ƙungiyoyin marubuta da ɗaiɗaikun mutane daban-daban.

A nata ɓangaren, Ƙungiyar Matasan Marubuta ta Najeriya (SYNY), taya murna ta yi gare su, bisa gagarumar nasarar da suka samu. A wani jawabi da shugaban ƙungiyar, Wole Adedoyin ya fitar, ya ce: “A matsayinmu na ƙungiyar da ta sadaukar da kanta wajen rainon matasan marubuta a Najeriya, muna alfahari da nasarar da Dokta Obari Gomba, Mista Henry Akubuiro da Mista Abideen Abolaji Ojomu suka samu. Wannan nasara da suka samu, abu ce mai ƙarfafa gwiwa ga marubuta masu tasowa, wajen yi masu jagora zuwa maida hankali ga ayyukan ƙirƙira domin samun ɗaukaka.

“Ƙungiyarmu na taya marubutan uku fatan samun kyakkyawar nasara a ƙarshen gasar, inda za a fidda zakara. Kasancewar wannan gasa tana da kyakkyawan tarihi dangane da ɗaga martabar nagartattun ayyukan adabi, muna da yaƙinin cewa, duk wanda ya yi nasarar zama zakara daga cikin waɗannan zaƙaƙuran marubuta uku, zai cancanci duk wata Karramawa daga wajenku.”

Ita dai wannan gasa da Kamfanin NLNG ke ɗaukar nauyin gudanarwa duk shekara, tana karrama zakaran da ya zo na ɗaya da kyautar Dala dubu 100.

A gasar ta bana, adadin littattafan wasan kwaikwayo 143 suka fafata, inda marubuta uku suka yi nasarar zuwa shingen ƙarshe. Kamar yadda kwamitin gasar ya bayyana, za a sanar da zakaran zakaru a ranar 13 ga Oktoban bana, a wani ƙwarya-kwaryan biki.
~~~~~~~~

Previous Post

Littafin Bango Ya Tsage: Takaitaccen Tsokaci Da Shawara

Next Post

NASIHAR JUMU’A: Daga Sheikh Aliyu Said Gamawa

Related Posts

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)
Adabi

SAKAMAKON ZAGAYE NA BIYU NA GASAR RUBUTU TA GIDAUNIYAR ZANNA-WALI (2025)

December 23, 2025
Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine
Adabi

Dalilan Da Suka Sanya Na Rubuta Littafin Tarihin Maitatsine

December 6, 2025
Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu
Adabi

Yau Take Juma’a: Allah Ka Albarkace Mu

December 5, 2025
Next Post
Lallai Hukuma Ta Tallafa Wa Marubuta Domin Yaƙar Jahilci – Sheikh Gamawa

NASIHAR JUMU'A: Daga Sheikh Aliyu Said Gamawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

Batutuwan Dubawa Game Da Kafa ’Yan Sandan Yanki

Batutuwan Dubawa Game Da Kafa ’Yan Sandan Yanki

May 16, 2025
True Christianity: A Powerful Insight

True Christianity: A Powerful Insight

September 24, 2023
Tarihin Ƙungiyar Hamas

Tarihin Ƙungiyar Hamas

October 13, 2023
Yadda Bikin Ƙaddamar da littafin SIRRIN MACE MUSULMA Ya Gudana A Kabo

Yadda Bikin Ƙaddamar da littafin SIRRIN MACE MUSULMA Ya Gudana A Kabo

May 29, 2025

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • BINCIKE: Zahirin Abin Da Ke Faruwa A BBC Hausa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation
  • Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco
  • Hukunta Ɗan T+adda Victor Solomon: Madalla Da Gwamnatin Jihar Kaduna

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

Tafawa Balewa, Sardauna And 15th January: A Day of Lamentation

January 15, 2026
Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

Gasar Kofin Afrika: Yau Take Tsakanin Nigeria Da Morocco

January 14, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.