YAMTARAWALA Ya Kama Hanyar Lashe Gasar Adabi Ta NLNG
Littafin wasan kwaikwayo mai taken “Yamtarawala – The Warrior King (Yamtarawala – Jarumin Mayaƙin Sarki) ya kama hanyar lashe Gasar Adabi ta bana, wadda Kamfanin Sarrafa Iskar Gas na Najeriya (NLNG Limited) ke shiryawa duk shekara.
Littafin, wanda marubuci kuma ɗan jarida Henry Akubuiro ya rubuta, ya samu nasarar tsallake shingen alƙalan gasar, inda ya kasance ɗaya daga cikin uku da za su fafata domin fitar da na ɗaya da na biyu da kuma na uku.
A ranar Talatar da ta gabata (29-08-2023) ce, Shugabar Kwamitin Gasar, Farfesa Akachi Adimorah ta sanar da sunayen littattafan guda uku. Sauran biyun sun haɗa da littattafan wasan kwaikwayo mai taken “For Grit” na marubuci Obari Gomba da kuma “The Ojuelegba Crossroads” wanda Abideen Abolaji Ojomu ya rubuta.
Kamar yadda kwamitin ya bayyana ingancin littattafan uku da suka yi nasara, ya ce tsarin wasannin kwaikwayon sun ciri tuta, musamman ta fuskar zubi da tsari, zaɓen kalmomin da suka dace da al’ada da kuma ingancin labari, wanda za a iya nunawa a aikace, a fim ko a daɓe. Ya ƙara da cewa littattafan sun cancanci ƙima ta musamman, a fagen adabi, waɗanda suka haɗa dukkan wata ƙwarewa a sarrafa alkalami da hikima, irin dai wadda kwamitin na Gasar Rubutun Adabi ta Najeriya ke buƙata.
Shugabar Kwamitin ta ce, alƙalan gasar sun yaba wa littafin “For Grit” da cewa babban wasan kwaikwayo ne da ya gamsar fiye da ƙima. Tsarin warware jigon labarin yana kama hankali, tsarin bugun littafin ya ƙayatar sosai.
Game da littafin “The Ojuelegba Crossroads” kuwa Farfesa Akachi ta ce alƙalan sun gamsu da shi sosai. Sun ce ya kawo bayanan da suka danganci zamantakewar al’umma da siyasa. Irin yadda marubucin ya tunkari bayyana faɗi-tashin al’umma na yau da kullum, da yadda suke ɗaukar matakan daidaita rikitattun al’amuran rayuwarsu domin dacewa, su ne suka inganta littafin, suka ba shi babbar daraja.
Da Shugabar Kwamitin ta zo bayani game da littafin “Yamtarawala – The Warrior King” na Henry Akubuiro kuwa, cewa ta yi: “Littafin ya ɗauki hankalin alƙalan gasar saboda tsarinsa mai hawa da sauka da nuna gwanintar wasan kwaikwayo. Yadda aka tsara shi bisa dacewa da inganci, zai sauƙaƙa ɗabbaƙa shi a aikace, a daɓe ko ma a allon fim. Irin yadda marubucin ya warware ƙunshiyar labarin, yana riƙe mai karatu cikin ƙayatarwa da saka nishaɗi.”
Baya ga kwamitin shirya gasar, marubutan uku da suka yi nasara sun samu yabo da jinjina daga ƙungiyoyin marubuta da ɗaiɗaikun mutane daban-daban.
A nata ɓangaren, Ƙungiyar Matasan Marubuta ta Najeriya (SYNY), taya murna ta yi gare su, bisa gagarumar nasarar da suka samu. A wani jawabi da shugaban ƙungiyar, Wole Adedoyin ya fitar, ya ce: “A matsayinmu na ƙungiyar da ta sadaukar da kanta wajen rainon matasan marubuta a Najeriya, muna alfahari da nasarar da Dokta Obari Gomba, Mista Henry Akubuiro da Mista Abideen Abolaji Ojomu suka samu. Wannan nasara da suka samu, abu ce mai ƙarfafa gwiwa ga marubuta masu tasowa, wajen yi masu jagora zuwa maida hankali ga ayyukan ƙirƙira domin samun ɗaukaka.
“Ƙungiyarmu na taya marubutan uku fatan samun kyakkyawar nasara a ƙarshen gasar, inda za a fidda zakara. Kasancewar wannan gasa tana da kyakkyawan tarihi dangane da ɗaga martabar nagartattun ayyukan adabi, muna da yaƙinin cewa, duk wanda ya yi nasarar zama zakara daga cikin waɗannan zaƙaƙuran marubuta uku, zai cancanci duk wata Karramawa daga wajenku.”
Ita dai wannan gasa da Kamfanin NLNG ke ɗaukar nauyin gudanarwa duk shekara, tana karrama zakaran da ya zo na ɗaya da kyautar Dala dubu 100.
A gasar ta bana, adadin littattafan wasan kwaikwayo 143 suka fafata, inda marubuta uku suka yi nasarar zuwa shingen ƙarshe. Kamar yadda kwamitin gasar ya bayyana, za a sanar da zakaran zakaru a ranar 13 ga Oktoban bana, a wani ƙwarya-kwaryan biki.
~~~~~~~~













