MALAM SULE LAMIDO:
Jagoran Talakawa Ya Cika Shekaru 78

__________
A ranar Lahadi mai zuwa, ɗimbin masoya ‘yan uwa da abokan arziki da ma abokan siyasar gwarzon ɗan kishin ƙasa, jigon siyasar Najeriya, Dakta Sule Lamido CON, za su yi kwamba a garin Dutse, Babban Birnin Jihar Jigawa, domin taya shi murnar cika shekaru 78 da haihuwa.
Mutum mai muhibba da martaba amma mai sauƙin kai, wannan fitaccen ɗan siyasar masu ra’ayin ci gaba, ya tabbata jajirtacce, mai sadaukar da kansa ga aikin gina Najeriya.
Ɗan siyasa mai himma da tsayayyen ra’ayin gina al’umma, daraja zaman lafiya mai ɗorewa, haɗin kai da kwanciyar hankalin ƙasa, Alhaji Sule ya amsa sunansa a zukatan miliyoyin ‘yan Najeriya.
A halaye da ɗabi’a, ya ci gaba da kasancewa mai aminci, amana da biyayya ga jam’iyyar da shi da wasu kamar Cif Solomon Daushep Lar da Mista Sunday Awoniyi da Alhaji Muhammad Abubakar Rimi, tare da sauran ’yan uwansu ’yan kishin ƙasa suka yi amfani da ita wajen korar sojoji daga mulki a shekarar 1999.
Ƙungiyarsu ta G34, wacce daga baya ta rikiɗe zuwa PDP, ita ce ta karɓi mulki daga hannun sojoji. Lamido ya ci gaba da kasancewa a cikin jam’iyyarsa ta PDP duk da matsaloli da dama, barazana da tsoratarwa, da kuma wasu ƙawancen siyasa marasa kyau da wasu ’yan jam’iyyar suka ƙulla da jam’iyyar da ke mulki, musamman ta hannun wasu wakilai da Abuja ke mara wa baya; abubuwan da suka haifar da watsewar ’ya’yan jam’iyyar na gaskiya zuwa wasu sansanonin siyasa.
Ana sa ran bikin ranar Lahadin nan, wanda aka shirya domin girmama tsohon ɗan Majalisar Wakilai ta Tarayya a Jamhuriya ta Biyu – Lamido, zai kasance babban biki.
Alhaji Lamido, a matsayinsa na ɗalibin siyasar Malam Sa’adu Zungur da Malam Abba Maikwaru da Malam Illa Ringim, tun sama da shekaru 50 da suka gabata, ya kasance mai ingantaccen tarihin zaman lafiya da kowa – ba shi da abokin gaba a siyasance da kuma mu’amala.
Jagoran Talakawa Lamido, Allah ya azurta shi da halayen son jama’a, yafiya, tausayi da kyakkyawar mu’amala da mutane. Ko yana kan kujerar gwamnati ko ba ya kanta, yana halartar bukukuwan aure na manya da ƙanana, yana zuwa bukukuwan ƙaddamar da ayyuka, sannan yana zuwa gaisuwar ta’aziyya ga kowane irin mutum, ba tare da la’akari da ƙabila, addini ko ra’ayin siyasa ba.
A yayin wannan gagarumin biki, Farfesa Nu’uman Muhammad Habib ne zai gabatar da jawabin buɗe taro, yayin da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Ahmad Muhammad Makarfi, CON, zai jagoranci taron. Babban mai gabatar da jawabi, Dakta Awwal Anwar, zai yi tsokaci ne mai taken: “Gina Sabuwar Najeriya: Jagorantar Matasa Bisa Hanyar Ingantacciyar Siyasa Mai Bin Ƙa’ida da Tsari.” Farfesa Kamilu Sani Fagge da Dakta Akilu Indabawa, su ne masu tattaunawa kan wannan batu.
Muna amfani da wannan dama wajen yi wa Kwamared Sule Lamido fatan ƙarin shekaru masu yawa cikin ƙoshin lafiya da wadata, domin ya ci gaba da yi wa bil’adama hidima.
Allah ya ƙara maka lafiya, ya kuma tsawaita maka rayuwa mai albarka, Baba.
_________












