Tambayoyin Neman Sani A Kan Littafin:
JAWAHIRUL MA’ANI

•••••••
Maganar gaskiya, tun ina yaro ƙarami, sama da shekara 50 da suka wuce na fara jin bayanai daban-daban game da mashahurin littafin nan mai suna #JAWAHIRUL MA’ANI. Wasu labarun na yabo ne da karrama shi, wasu kuwa akasin haka.
Wani abin da ke ƙara jan hankalina game da littafin nan shi ne, yadda na ga a kullum na wayi gari, sai na ci karo da inda ake maganarsa. Ga shi kuma duk da irin ƙwazzabar son karatuna amma har yanzu ban samu damar karanta shi ba. Wannan dalili ne ma ya sanya na ce bari in baza komar tambaya a wannan saha, domin a ƙara mani bayani kuma da sani, dangane da wannan littafi.
Don haka, ina son don Allah wanda ya karanta littafin nan ko kuma yake da masaniya ta haƙiƙi a kansa, ya ƙara mani bayani. Ga tambayoyin nawa:
√ Shin ka taɓa karanta littafin Jawahirul Ma’ani kuma me ka fahimta daga abin da ka karanta?
√ Idan ba ka karanta ba, shin ko ka taɓa sauraren bayani daga wani malami da ya karanta shi?
√ Shin me ka fahimta game da wannan littafi na Jawahirul Ma’ani?
√ Don Allah ko a ina zan iya samun wannan littafi na sayarwa?
SANARWA: Kamar yadda na bayyana a baya, na bijiro da waɗannan tambayoyi ne domin neman bayani da ƙarin ilimi. Don haka, don Allah idan mutum bai da sanin amsa ko ɗaya, kada ya ce zai magana ko kawo wani bayani akasin tambayoyin nan.
_______________













