HUJJA MAGANIN HAYANIYA – 1

__________
Rayuwar duniya tana da ƙalubale da yawa, sai dai kuma idan aka gudanar da ita bisa ilimi da fahimta, za a samu fa’ida ba ‘yar kaɗan ba.
Ta yaya za a kauce wa ruɗani da hayaniya a yayin mu’amala da cuɗanya da mutane, dabbobi, tsirrai da sauran halittun da Allah ya samar a doron ƙasa? Amsa ita ce, ta hanyar ilimi da biɗar hujjar tafiyar da rayuwa.
A yayin da Allah ya halitta mutum kuma ya halitta dukkan halittun duniya, sannan ya shugabantar da shi mutum a matsayin halifansa a bayan ƙasa, bai bar shi haka nan babu jagora ba. Ya ba shi ilimi da littafi da manzanni a matsayin jagora/malamai, domin bayyana masa HUJJA da ƘA’IDOJIN da zai mu’amalanci ‘yan uwansa mutane da ma sauran halittun da yake gani a muhallinsa.
__________












