SASSANYAN AMINCI (6)
(Diwanin Bashir Yahuza Malumfashi)

_______________
32
Al’umma mun gode Allah,
Mun shaida kai ne Jallah,
Kai ne mai ba da falala,
Kai ne mai kore wahala,
Ka ba mu Manzo babba.
33
Jama’a mu ƙara godiya,
Lallai kam kar mu gajiya,
Dare rana duka safiya,
Mu daddage ba sanya,
Bautar Allah mai Ka’aba.
34
Mu sani mu duk bayi ne,
Na Allah Khaliƙi ne,
Mu mutane har aljanu ne,
Aikinmu yin bauta ne,
Ga Allah ba kankanba.
35
Shi ne mai amsar tuba,
Shi ne kuma ya hana gaba,
Ya haramta aikin tsatsuba,
Har da aikin mai yin zamba,
Gaskiyar zance ba wai ba.
(Za Mu Ci Gaba)
_______________
Akwai bayin Allah da suke taimakawa domin ganin nasarar an wallafa wannan Diwani, saboda ƙaunarsu ga Fiyayyen Halitta. Don haka, muuna addu’a ta musamman ga waɗannan bayin Allah (Masoya Manzon Allah – Saw), da suke taimaka wajen wannan aiki:
1-Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson).
2-Injiniya Muntari Sagir
3-Injiniya Tukur Tingilin.
4-Malam Labiru Musa Ƙafur.
5-Malam Haruna Musa Rugoji.
6-Dr. Aminu Waziri.
7-Abdul’aziz Abdul’aziz
8-Zainab Ahmad Mohammed.
Allah ya saka maku da mafificin alheri, ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa (saw), ya sa muna cikin cetonsa, Amin!
GUDUNMOWA:
Haka kuma, ƙofa a buɗe take ga dukkan al’umma masoya Manzon Allah, ga duk mai son saka jarinsa a wannan aiki, domin tarayya cikin lada, sai tuntuɓi Bashir Yahuza Malumfashi a wannan layin waya, kira ko Whattsap: 08065576011
Allah sa mu dace Amin!
_______________













