Matsalar Tsaro A Najeriya: Madalla Da Majalisar Dokokin Amurka
Daga Dr. Adam Abaji

•••••••
Yau zaman jin bahasin Majalisar Dokoki ta Amurka (Congressional Hearing) da aka gudanar a Washington DC ya zama wani muhimmin lamari a tattaunawar duniya game da matsalar tsaro a Najeriya.
A karon farko, bayan ɗaukar tsawon lokaci ana kai-komo da wannnan batu, a yau mun shaida tattaunawa mai ma’ana, wacce ta dogara da hujjoji, a gaban Majalisar Dokoki ta Amurka. Mambobi daga manyan jam’iyyu biyu sun yi tattaunawa mai zafi da kuma nuna damuwa kan halin da Najeriya take ciki, dangane da taɓarɓarewar al’amuran tsaro. Sun amince da cewa, akwai tsananin ta’addanci da kuma irin raɗaɗin da ’yan Najeriya ke sha a sassa daban-daban na ƙasar. Haka kuma sun fahimci yadda lamarin ya rikice, kamar yadda suka fahimci cewa akwai buƙatar taka-tsan-tsan dangane da irin matakan da ƙasashen waje za su iya ɗauka da sakamakon da hakan zai iya haifarwa.
Abin da ya fi ɗaukar hankali shi ne, yadda suka ƙi amincewa da duk wani yunƙurin kai tsaye na tura sojojin ƙasashen waje zuwa Najeriya. Maimakon haka, sun buƙaci a samar da haɗin kai mai ma’ana, cikin fahimta da ƙwarewa, tsakanin Gwamnatin Najeriya da ta Amurka. Sun ba da shawarar a yi haɗin gwiwa wajen tantance ƙarfin Najeriya a yaƙi da ta’addanci a halin yanzu. Sun ƙarfafi gwiwar Amurka da cewa ta taimaka ta ɓangaren samar da bayanan sirri (intelligence) tare da aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaron Najeriya, wajen bincikowa, tantancewa, kamawa ko kawar da ƙungiyoyin ta’addanci da ke haddasa ɓarna a sassan ƙasar.
Wannan ya haɗa da hare-haren ‘yan Boko Haram a Arewa maso Gabas da ayyukan ’yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya. Haka kuma da ƙungiyoyi masu tada hankali a Kudu maso Gabas da Kudu maso Yamma. Majalisar ta amince da bayanin da ke cewa, ’yan Najeriya ne gaba ɗaya suke shan wahala dangane da lamuran rashin tsaro, ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba. Kuma kowane ɗan Najeriya na da haƙƙin samun tsaro da mutunci.
Wannan sabon salo abin maraba ne matuƙa. Ya fi tsari, ya fi samar da natsuwa fiye da kiraye-kirayen baya da aka yi, na cewa a kai farmaki Najeriya. Wannan rashin tunani ne mai zurfi, domin hakan zai keta ’yancinmu na ‘yan ƙasa, sannan ya jefa rayukan fararen hula cikin haɗari. Yau mun ga wata hanya mai hikima, wadda ke mutunta Najeriya kuma take mai da hankali kan abin da ya fi dacewa. Wannan nasara ce ga diflomasiyya da duk waɗanda suka yi amanna da cewa haɗin kai mai kyau tsakanin ƙasashe ya fi tsoma bakin soji, wanda zai lalata lamurra.
Ya zama wajibi ga Gwamnatin Tinubu ta yi amfani da wannan dama. Ya kamata Najeriya ta hanzarta ƙarfafa haɗin gwiwa da Amurka da kuma ƙasashen Turai. Haka kuma dole mu fahimci wani saƙo mai muhimmanci da ya fito daga zaman Majalisar Dokokin Amurka na yau. Wannan kuwa ya haɗa da buƙatar da ke akwai ga Najeriya da ta yi gaggawar tura jakadu a muhimman ƙasashen waje. Mu gane cewa mutuncin Najeriya ya zube a idon duniya, sakamakon yaɗa bayanan ƙarya da yaudara. Muna buƙatar jakadu ƙwararru da za su tsaya tsayin daka, su kare muradunmu tare da hulɗa da shugabannin duniya, domin dawo da martabar ƙasarmu.
Haka kuma, lallai ne mu fahimta da cewa, wannan ba lokacin ba da muƙamai saboda alfarma ba ne. Lokaci ne na zaɓen mutanen da suka cancanta, mutanen da za su wakilci Najeriya cikin daraja, su yi aiki ba gajiyawa don ganin an samar da makoma mai kyau, wadda za ta samar mana da tsaro da wadata ga ’yan Najeriya duka.
Ga wasu ‘yan Najeriya da ke gida, waɗanda suka riƙa yin murna da yiwuwar a kai harin soja ga ƙasarsu, ina roƙon ku da ku sake tunani sosai. Za ku iya jin haushi ko takaici amma yana da muhimmanci ku tsaya ku yi nazari cikin nutsuwa. Irin wannan agaji na harin soja daga Amurka ko wata babbar ƙasa, ba zai gyara Najeriya ba. Harin zai halaka rayuka, ya ƙara taɓarɓara halin da muke ciki. Wannan lokaci wata dama ce ta daban, domin haɗin gwiwa da manyan ƙasashe, su samar da goyon baya da bayanan sirri da za su kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a ko’ina cikin Najeriya.
Idan muka yi amfani da wannan dama da muhimmanci kuma muka yi aiki da abokan hulɗa masu dacewa, wannan na iya share mana hanyar magance matsalolinmu. Wannan ne lokacin da Najeriya za ta tashi da mutunci, ƙarfi da haɗin kai. Lokacin da gwamnati za ta samu goyon baya wajen kare ’yan ƙasa da kiyaye ’yancin ƙasarmu. Lokaci ne da Najeriya za ta fara hikimar ɗagawa sama, maimakon a bar ta a ƙuryar baya
._______________
Dr. Adam Abaji, babban malami ne a Jami’ar Alberta, Canada (Wannan tsokaci, asalinsa da Ingilishi ne, muka fassara zuwa Hausa).












