SASSANYAN AMINCI (5)
(Diwanin Bashir Yahuza Malumfashi)

__________
27
Ga Kilabi yana a cikinsu,
Ga Ƙusayyu duk a gidansu,
Abdulmanafi akwai shi cikinsu,
Hashimi yana bayansu,
Kakannin Manzo babba.
28
Ga mutane masu muhibba,
Jiddadun muna ta maraba,
Ba mu so fa mu saɓa lamba,
Ko mu zam cikin tababa,
Allah kare mu daga jaraba.
29
Abdulmuɗallabi ka cika jarumi,
Ka tsere wa gararumi,
Abadan ba ka shiga zullumi,
Ba ka shayin duk azzalumi,
Ko wani gungun ‘yan daba.
30
Kaf mu tashi mu yi masa jinjina,
Ga bango babba na jingina,
Baban Manzo mai yakana,
Abdullahi mai kashe fitina,
Ka yi alheri shi ka saba.
31
Kai ne ka haifo Manzo,
Duniya a ranar da yaz zo,
Sai haske babu ɗan hazo,
Mustapha Muhammadu Manzo,
Rahama ne shi ba kaɗan ba.
(Za Mu Ci Gaba)
__________
Akwai bayin Allah da suke taimakawa domin ganin nasarar an wallafa wannan Diwani, saboda ƙaunarsu ga Fiyayyen Halitta. Don haka, muuna addu’a ta musamman ga waɗannan bayin Allah (Masoya Manzon Allah – Saw), da suke taimaka wajen wannan aiki:
1-Alhaji Jibrin Sama’ila (Jibson).
2-Injiniya Muntari Sagir
3-Injiniya Tukur Tingilin.
4-Malam Labiru Musa Ƙafur.
5-Malam Haruna Musa Rugoji.
6-Dr. Aminu Waziri.
7-Abdul’aziz Abdul’aziz
8-Zainab Ahmad Mohammed.
Allah ya saka maku da mafificin alheri, ya ƙara mana ƙaunar Manzonsa (saw), ya sa muna cikin cetonsa, Amin!
GUDUNMOWA:
Haka kuma, ƙofa a buɗe take ga dukkan al’umma masoya Manzon Allah, ga duk mai son saka jarinsa a wannan aiki, domin tarayya cikin lada, sai tuntuɓi Bashir Yahuza Malumfashi a wannan layin waya, kira ko Whattsap: 08065576011
Allah sa mu dace Amin!
_______________













