• About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact
Friday, August 14, 2026
  • Login
Taskar Gizago
Advertisement
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna
Taskar Gizago
No Result
View All Result
Home Siyasa

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

SHARHI

Bashir Yahuza Malumfashi by Bashir Yahuza Malumfashi
July 24, 2026
in Siyasa
0
Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya

Gwamna Yahaya da Sheikh Pantami

18
VIEWS
Share on FacebookShare on TwitterWhatsappEmail a Friend

Siyasar Gombe Ta Kacame Tsakanin Pantami Da Gwamna Yahaya
__________
Kamar yadda Shafin Northern Nigeria Hub a intanet ya ruwaito, tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, kuma ɗan takarar Gwamnan Jihar Gombe na jam’iyyar PDP, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami, ya mayar da martani mai zafi kan suka da ake yi dangane da fara yaƙin neman zaɓe da wuri, inda ya bayyana cewa tsoratarwa da barazanar da hukumomin gwamnati ke yi, alama ce ta cewa tafiyarsu na dab da samun nasara.

Gwamna Yahaya da Sheikh Pantami

Da yake jawabi ga magoya bayansa a cikin wani faifan bidiyo da ya bayyana a baya-bayan nan, Sheikh Pantami ya yi watsi da yunƙurin da abokan hamayyarsa ke yi na tsoratar da magoya bayansa, ta hanyar amfani da hukumomin tsaro. Ya jaddada cewa tsangwamar siyasa ko barazanar ɗauri ba za su hana su ci gaba da tafiyarsu ba.

Related posts

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

July 8, 2026
Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

June 17, 2026

“Da zarar ka kalli waɗannan idanuwan, za ka san ba za a iya razana mu da barazana ba,” in ji Pantami. “Idan ka fara wata tafiya kuma aka fara yi maka tsoratarwa, wannan alama ce ta cewa nasara na gabatowa. Bayan na yi rashin mahaifina, mahaifiyata, ɗana da sauran makusantana, babu abin da ya rage a duniya da zan ji tsoro a kansa.”

Pantami ya kuma ƙalubalanci abokan hamayyarsa, musamman shugabanninsu, da su daina yin maganganu a fakaice, su fito fili domin gudanar da muhawara ido-da-ido, tare da gabatar da hujjoji ga al’ummar Jihar Gombe.

“Idan ba ku yarda da abin da muke faɗa ba, kada ku tsaya gefe kuna magana. Ku aiko da gayyata a hukumance, mu haɗu ido-da-ido, jama’a su gani waye ke da hujjoji na gaskiya,” in ji shi.

Kalaman Pantami sun zo ne a matsayin martani a fakaice ga wani jawabi da Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi a baya. A lokacin da yake magana kan dokokin yaƙin neman zaɓe. Gwamna Inuwa Yahaya ya soki wasu ‘yan siyasa da ya zarga da karya ƙa’idojin Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), ta hanyar fara yaƙin neman zaɓe kafin lokacin da doka ta tanada, tare da yaudarar jama’a.

A cikin jawabinsa, Gwamna Yahaya ya kuma yi tsokaci kan dogon tarihinsa na ilimi da tarbiyya a Jihar Gombe, musamman a fannin ilimin addinin Musulunci. Ya bayyana cewa tun kafin siyasar zamani ta samu karɓuwa, shi Alaramma ne, yana mai nuna cancantarsa da matsayinsa a tsakanin al’umma.

Kodayake Gwamna Yahaya bai ambaci sunan Sheikh Pantami kai tsaye ba, masu sa ido kan harkokin siyasa sun ɗauki kalamansa kan fara yaƙin neman zaɓe da kuma cancantar ilimin addini a matsayin martani kai tsaye ga tarurruka da jawaban da Pantami ke yi a sassa daban-daban na jihar.

Sabbin kalaman Pantami sun nuna cewa takun-saƙar siyasa a Jihar Gombe tana ƙara ɗaukar zafi, yayin da ɓangarorin biyu ke ci gaba da amfani da kalamai masu ƙarfi a daidai lokacin da ake tunkarar fafatawar siyasa mai zuwa.
__________

Previous Post

Saƙon Godiya Da Bangajiya

Next Post

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

Related Posts

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti
Siyasa

Zaɓen 2027: Akwai Yiwuwar Farfesa Pantami Ya Yi Nasara – Farfesa Lawanti

July 8, 2026
Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya
Siyasa

Jaafar Jaafar Ya Buɗe Idanun ‘Yan Kwankwasiyya

June 17, 2026
Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi
Siyasa

Minista Dr. Muttaqha Rabe Darma Kana Bi Na Bashi

April 22, 2026
Next Post
General Buratai to Marry Off His Daughter Today

General Buratai to Marry Off His Daughter Today

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

RECOMMENDED NEWS

RAMADAN KARIM: 30-1447

RAMADAN KARIM: 30-1447

March 19, 2026
Kar Nake Ganin Ka

Kar Nake Ganin Ka

May 29, 2023
Akwai Yiwuwar Spain Za Ta Lashe Kofin Duniya Na Bana

Akwai Yiwuwar Spain Za Ta Lashe Kofin Duniya Na Bana

July 18, 2026
Rage Raɗaɗin Talauci: Attajirai Ku Yi Koyi Da Sabi’u Mahuta

Rage Raɗaɗin Talauci: Attajirai Ku Yi Koyi Da Sabi’u Mahuta

August 7, 2023

FOLLOW US

BROWSE BY CATEGORIES

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

POPULAR NEWS

  • Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    Gwamnan Katsina Ya Ƙi Amsar Kyautar Raguna 100 Daga Hannun Attajiri

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Ta Tsinci Naira Miliyan 60 A Saudiyya Ta Miƙa Wa Hukuma

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • LUWAƊI DA YARA 14: Yadda Aka Bankaɗo Asirin Kabir Ɗan Hisba

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sojojin Najeriya Sun Kama Makashin Sarkin Gobir

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Tarihin Waƙar Yaƙin Tabuka

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Taskar Gizago

Follow us on social media:

Recent News

  • Our Daily Message
  • Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina
  • Gwamnati Za Ta Samar Da Ingantaccen Tsarin Gudanar Da Makarantun Alƙu’rani A Jihar Katsina

Category

  • Adabi
  • Addini
  • Babban Labari
  • Barkwanci
  • Dausayin Kauna
  • ENGLISH
  • Gizago
  • Gumbar Dutse
  • Hotuna
  • Labarai
  • Nishadi
  • Noma Da Kiwo
  • Sarauta
  • Shanshani
  • Sharhi
  • Sinadarin Rayuwa
  • Siyasa
  • Ta'aziyya
  • Wasanni

Recent News

Our Daily Message

Our Daily Message

August 14, 2026
Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina

Regulation, Standardisation of Qur’anic Schools Under Way in Katsina

August 13, 2026
  • About us
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
  • Sharhi
  • Gumbar Dutse
  • Dausayin Kauna
  • Gizago
  • Sarauta
  • Sinadari
  • Adabi da Nishadi
  • Barkwanci
  • Shanshani
  • Hotuna

© 2023 Taskar Gizago - Ilimi da Nishadi

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
This website uses cookies. By continuing to use this website you are giving consent to cookies being used.